Connect with us

News

EFCC Ta Girke Jami’ai A Wurin Zaben Dan Takarar Shugaban Kasar APC

Published

on

Daga kabiru basiru fulatan 

 

Advertisement

 

Hukumar Yaki da Karya Tattalin Arziki ta Kasa (EFCC) ta girke jami’anta domin sanya ido kan zaben fitar da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC da ke gudana a Abuja.

Advertisement

 

Wakilan mu  sun ga jami’an na EFCC sun ga yadda jami’an hukumar suke kai-komo a wurin taron da ke gudana a Dandalin Eagles Square a birnin Abuja.

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Duk da cewa taron bai kankama ba, ana ganin hallarar jami’an hukumar a wurin taron na da nasaba da zargin hada-hadar kudade da sunan sayen daliget a lokacin tarukan zaben ’yan takara.

Advertisement

 

A ranar Talata ne dai jam’iyyar APC mai mulkin Najeriya take fara gudanar da babban taronta da zaben dan takararta na kujerar shugaban kasa a zaben 2023.

Advertisement

 

Kawo yanzu dai ana ta kiki-kaka kan wanda jam’iyyar za ta fitar, inda gwamnonin Arewa ke son a bai wa yankin Kudanci, a yayin da wadansu daga cikin masu neman kujerar daga yankin Arewa suka ce ba za ta sabu ba.

Advertisement

An Ceto Mahaifiyar Dan Takarar Sanata A Kano Daga Hannun ’Yan Bindiga

Ya zuwa wannan lokaci dai sai sake lale jam’iyyar take yi a kan batun fitar da dan takara babu hammaya, lokacin fara gudanar da zaben kuma sai kara karatowa yake ta yi.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending