Opinion
Idan Har Kalashnikov Ya Yi Nadamar Kirkirar AK-47, Najeriya Ma Za Ta Iya Dakile Tashin Hankalin Siyasa
A shekara 27, Mikhail Kalashnikov ya kirkiri abin da daga baya ya zama daya daga cikin shahararrun bindigogin yaki a tarihin zamani, wato AK-47. A matsayinsa na soja kuma injiniya dan kasar Tarayyar Soviet a lokacin, Kalashnikov ya kirkiro makamin ne a lokacin Yakin Duniya na Biyu domin kare kasarsa daga mamaya. Bisa tarihin da aka sani, manufarsa ita ce kare kasa, ba yada hallaka a duniya ba.
Abin da ya bambanta AK-47 shi ne saukin amfani da ita, juriyarta da kuma yadda ake iya sarrafa ta cikin sauki. Bindigar na aiki ko da a cikin mawuyacin yanayi, tana da saukin amfani da gyarawa, sannan tana aiki yadda ya kamata a wurare masu wahala. Wadannan siffofi suka sa ba sojojin kasashe kadai suka rungume ta ba, har ma kungiyoyin masu dauke da makamai a sassa daban daban na duniya. Tsawon shekaru, kasashe da masana’antun makamai daban daban sun rika gyara da daidaita fasaharta domin bukatun tsaro da yaki, abin da ya sa ta zama daya daga cikin bindigogin da suka fi yaduwa a duniya.
Iran Ta Mayar Da Martani Ga Masu Shiga Tsakani Na Pakistan Kan Shawarar Amurka Ta Kawo Ƙarshen Yaƙi
Yau, kusan shekaru tamanin bayan kirkirarta, AK-47 da ire irenta har yanzu suna daga cikin manyan makaman da ake amfani da su a rikice rikice a fadin duniya. Abin takaici, ‘yan bindiga, ‘yan ta’adda, masu tayar da kayar baya da kungiyoyin masu aikata laifuka a sassa daban daban na Afirka da sauran duniya na ci gaba da amfani da bindigar wajen tada hankali, rusa al’umma da kashe bayin Allah marasa laifi.
Sai dai duk da shahararsa a matsayin wanda ya kirkiri wannan bindiga, an rawaito cewa Kalashnikov ya nuna nadama sosai kan irin barnar da makamin ya haddasa kafin rasuwarsa a shekarar 2013 yana da shekaru 94. An ce ya taba bayyana cewa da ma gara ya kirkiri wata na’urar noma ko samar da abinci maimakon bindigar da aka alakanta da zubar da jini da barna tsawon shekaru.
Wannan tunani na Kalashnikov na dauke da babban darasi ga al’ummomi, musamman Najeriya.
Rikicin siyasa da matasa ke aikatawa a karkashin sunan siyasa ya ci gaba da jefa tarihi, zaman lafiya da martabar jihohi da dama a Najeriya cikin matsala. A wasu jihohi, abin da ya fara a matsayin hamayya ta siyasa yanzu ya rikide zuwa daba, tsoratarwa, sata, lalata dukiyoyi da kai hare hare kan bayin Allah masu neman halal.
Daya daga cikin manyan masifun siyasar Najeriya shi ne yadda wasu marasa kishin kasa ke amfani da matasa marasa galihu da aikin yi a matsayin kayan fada na siyasa. Lokacin zabe ko rikicin siyasa, ana daukar wadannan matasa, a basu makamai, a rude su da alkawuran kudi da kariya ko mukamai da yawanci ba sa tabbata.
Abin takaici kuwa, mafi yawan ‘yan siyasar da ke daukar nauyin tashin hankali ba za su taba bari ‘ya’yansu su shiga irin wadannan ayyuka ba. ‘Ya’yansu suna zuwa kasashen waje domin karatu a manyan jami’o’i da gina rayuwa mai kyau, yayin da ‘ya’yan talakawa ake jefawa cikin kangin rayuwar daba da tashin hankali.
Wannan munafunci dole ne a fuskance shi da gaskiya.
Dimokuradiyya ba yaki ba ce. Siyasa bai kamata ta zama hanyar daukar mutane zuwa aikata laifi ba. Ya kamata zabe ya kasance bisa hujjoji, tattaunawa, manufofi da iya jan hankali ta hanyar magana, ba tashin hankali, tsoro da zubar da jini ba. Duk wata siyasa da ke ci gaba da haifar da matasa masu tashin hankali tana gina matsalar tsaro ce ga kanta a nan gaba.
Illar kirkirar ‘yan daba na siyasa tana da yawa.
Matashin da aka saba da tashin hankali saboda siyasa yau na iya zama dan fashi da makami, mai garkuwa da mutane, dan kungiyar asiri, dillalin miyagun kwayoyi ko ma dan ta’adda gobe. Tashin hankali ba ya karewa bayan zabe. Da zarar makamai da kungiyoyin ta’addanci sun zama ruwan dare, al’umma kan rasa iko. Garuruwa su zama marasa tsaro, kasuwanci ya durkushe, masu zuba jari su gudu, tattalin arziki kuma ya lalace.
Mafi muni ma shi ne, daba ta siyasa tana lalata tarbiyyar al’umma. Tana koya wa matasa cewa tashin hankali hanya ce ta samun kudi, suna da daukaka. Tana rage darajar doka, tana karfafa rashin hukunta masu laifi, tare da rage amincewar jama’a da dimokuradiyya.
Najeriya ba za ta iya ci gaba da tafiya a wannan hanya ba.
Dole ne a sanya iyaka kan amfani da matasa a matsayin kayan tashin hankali.
Malamai, sarakuna, iyaye, kungiyoyin fararen hula, ‘yan jarida da masu kishin kasa a siyasa dole su hada kai wajen kin amincewa da daba ta siyasa. Dole ne a rika fallasa da hukunta ‘yan siyasar da ke daukar nauyin tashin hankali.
A lokaci guda kuma, gwamnati dole ta wuce fadin baki ta magance tushen matsalar da ke tura matasa zuwa tashin hankali kamar talauci, rashin aikin yi, shaye shayen miyagun kwayoyi da jahilci.
Ana bukatar mafita mai dorewa da wayewa. Saboda nauyin da ke kan gwamnati, jihohi a Najeriya ya kamata su yi tunanin kafa asusun hadin gwiwar jama’a domin tsaro da cigaban matasa, wanda zai kasance a bayyane kuma ba tare da tsoma bakin siyasa ba. Wannan tsari ya kamata ya hada masu zaman kansu, kungiyoyin fararen hula, kwararru, malamai da wakilan al’umma domin tabbatar da gaskiya da amincewar jama’a. Amma kafin hakan, dole a fara gagarumin wayar da kai.
Irin wadannan asusu za su iya mayar da hankali kan,
Taimaka wa shirye-shiryen tsaron al’umma,
Gyaran hali da tallafa wa matasan da tashin hankali ya lalata,
Samar da horon sana’o’i, tallafin karatu da jari ga matasa,
Kara yawan cibiyoyin kula da lafiyar kwakwalwa da gyaran masu shaye shaye,
Shirya wasanni, kirkire kirkire da shirye shiryen wayar da kan matasa kan hakkin kasa,
Karfafa tattara bayanan sirri da hanyoyin hana rikici kafin ya barke.
Idan jama’a suka yarda cewa ana gudanar da kudade cikin gaskiya kuma ana amfani da su wajen inganta tsaro da rayuwar matasa, to za su fi bada goyon baya da gudummawa.
Ya kamata a duba matasan Najeriya a matsayin ginshikan cigaban kasa, ba makaman siyasa ba. Najeriya na bukatar siyasar da ta ginu kan tunani, kwarewa, cigaba da shugabanci nagari, ba tashin hankali da amfani da talakawa ba. Ba za a iya gina makomar kasa ta hanyar lalata rayuwar ‘ya’yan talakawa yayin da ‘ya’yan masu fada a ji ke rayuwa cikin walwala a wasu kasashe ba.
Idan har Mikhail Kalashnikov ya iya nadamar kirkirar AK-47, to Najeriya bai kamata ta jira sai al’umma ta lalace kafin ta yi nadamar irin mummunar al’adar tashin hankalin siyasa da ake renowa a yau ba.
Abbas Ibrahim ya rubuto daga Kano, ana iya tuntubarsa ta wannan adireshin: abbasibrahim664@gmail.com
-
News7 days agoShekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano
-
News4 days agoKotu Ta Daure Wani Limamin Masallacin Juma’a Wata 1 Kan Tura Bidiyon Tsaraici Ga Matar Aure A Kano
-
News6 days agoƘalubalen Da Masu Ƙananan Sana’o’i Ke Fuskanta Saboda Ƙarancin Wutar Lantarki A Kano
