News
Al-Shabab na tursasa wa manoma biyan haraji a Somaliya
Daga Khadija abdullahi muhmd
Haraji mai tsanani da ƙungiyar al-Qaeda mai ƙawance da al-Shabab ta ƙaƙaba wa mutane a wasu yankunan Somaliya ya sa manoma ba sa iya girbe amfanin gonarsu a yayin da ake fama da matsannacin fari.
Zai yi wuya INEC ta iya yi wa ƴan Najeriyar da ke son yin katin zaɓe rijista’
Za’a Yi Jigilar Maniyyata Aikin Hajjin Kaduna 2491 Zuwa Ƙasa Mai Tsarki
Abdirahman Abdishakur Warsame, jakada na musamman ga shugaban ƙasar Hassan Sheikh Mohamud a kan batun farin, ya ce harajin na al-Shabab na tursasa wa manoma tserewa su bar gonakinsu da gidajensu.
Mr Warsame ya shaida wa shugaban ƙasar da shugabannin gundomomin ƙasar hakan ne a jiya Lahadi a wani taro da aka shafe kwana biyu ana yi.
Ya ce fiye da ƴan Somaliya miliyan bakwai ne fari ya shafa. Kuma mutum 250,000 daga cikinsu na fuskantar matsananciyar yunwa.
Al-Shabab na yawan amfani da yunwa da ake fama da ita a ƙasar don ƙara fito da kanta da kuma bayar da tallafi ga jama’a.
Source BBC
-
News2 days ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion6 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News2 days ago
Zaben 2027: INEC Ta Amince Da Atiku Abubakar, ‘Yan Takarar ADC 470
