News
Babu Me Yi Wa Buhari Katsa-Landan A Mulkinsa — Fadar Shugaban Kasa
Daga Sulaiman ado Ahmed
Fadar Shugaban Kasa ta ce Shugaba Muhammadu Buhari ne ke daukar kowanne irin mataki a kashin kansa, ba tare da wani ya tilasta shi ko ya yi masa katsa-landan ba.
An yi karin kudin gas a kasar Saudiyya
Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun Shugaban, Malam Garba Shehu, ya fitar a ranar Talata.
Kazalika, sanarwar ta ce, “Shugaba Buhari na daukar matakansa ne kuma ya aiwatar da su ba tare da wasu da ake wa kallon ’yan hana-ruwa gudu ba sun tsoma masa baki.”
Sanarwar na zuwa ne bayan da ake rade-radi a kafafen yada labarai cewar wasu na yin uwa da makarbiya a gwamnatin Shugaba Buhari.
Hakan ne ma a cewarsu ya sa har ya gaza zabar magajinsa a zaben fid-da gwanin Shugaban Kasa da jam’iyyar APC ta kammala.
Har wa yau, Fadar ta ce irin yadda aka gudanar da zaben na fid-da-gwanin dan takarar Shugaban Kasa a APC, ya nuna cewa Buhari Shugaba ne mai martaba dimokuradiyya duk da cewar shi tsohon soja ne.
-
News3 days ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion7 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News3 days ago
Zaben 2027: INEC Ta Amince Da Atiku Abubakar, ‘Yan Takarar ADC 470
