Connect with us

News

Babu Me Yi Wa Buhari Katsa-Landan A Mulkinsa — Fadar Shugaban Kasa

Published

on

Garba Shehu

Daga Sulaiman ado Ahmed 

 

 

 

 

Fadar Shugaban Kasa ta ce Shugaba Muhammadu Buhari ne ke daukar kowanne irin mataki a kashin kansa, ba tare da wani ya tilasta shi ko ya yi masa katsa-landan ba.

Advertisement

An yi karin kudin gas a kasar Saudiyya

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun Shugaban, Malam Garba Shehu, ya fitar a ranar Talata.

 

Kazalika, sanarwar ta ce, “Shugaba Buhari na daukar matakansa ne kuma ya aiwatar da su ba tare da wasu da ake wa kallon ’yan hana-ruwa gudu ba sun tsoma masa baki.”

 

Sanarwar na zuwa ne bayan da ake rade-radi a kafafen yada labarai cewar wasu na yin uwa da makarbiya a gwamnatin Shugaba Buhari.

Advertisement

 

Hakan ne ma a cewarsu ya sa har ya gaza zabar magajinsa a zaben fid-da gwanin Shugaban Kasa da jam’iyyar APC ta kammala.

 

Har wa yau, Fadar ta ce irin yadda aka gudanar da zaben na fid-da-gwanin dan takarar Shugaban Kasa a APC, ya nuna cewa Buhari Shugaba ne mai martaba dimokuradiyya duk da cewar shi tsohon soja ne.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending