Connect with us

News

Sojojin Najeriya sun gano ɗaya daga cikin ƴan matan Chibok

Published

on

Daga yasir sani Abdullah

 

Rundunar sojin Najeriya ta gano ɗaya daga cikin ƴan matan Chibok a Jihar Borno.

Akalla mutum 113 ne ‘yan bindiga suka kashe daga ranar 5 zuwa 11 ga Yunin 2022 a kasar nan.

A wani saƙo da rundunar ta wallafa a shafinta na Twitter, ta ce dakarun rundunar haɗin gwiwa ta 26 ne suka gano ta a lokacin da suke shawagi a kusa da garin Ngoshe a jiya Talata.

Sojojin dai sun ce sun ga Mrs Mary Ngoshe ne ɗauke da ɗanta kamar yadda suka wallafa hotonsu a shafinsu na Twitter.

Tun a Afrilun 2014 ne dai aka sace sama da ƴan matan na Chibok 270 sai dai sama da 100 an sako su wasu kuma sun tsere.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending