News
Za mu rinka tura malaman mu zuwa Algeria domin neman ilimi – Ganduje

Daga kabiru basiru fulatan
Gwamnan jihar Kano, Dr. Abdullahi Umar Ganduje, a shirye Kano ta ke ta hada hannu da kasar Algeria, domin inganta ilimi a jihar.
Dr Abdullahi Umar Ganduje ya tabbatar da hakan ne a lokacin da ya karbi bakwancin shugaban darikar Tijjaniyya na duniya, Ali Bel Arabi a fadar gwamantin Kano.
“Za kuma mu yi kokari wajen aiko malaman mu zuwa kasar Algeria, domin su rinka samun ilimi”. Inji Ganduje
Shi kuwa Sheikh Ali Abel Arabi, ya nuna jin dadin sa tare da godewa al’ummar Kano da Najeriya baki daya.