News
Yadda mahaifiyar Hanifah ta nannaushi malamin da yai garkuwa da kashe ƴar ta a Kano
Daga kabiru basiru fulatan
Mahaifiyar Hanifah Abubakar, ƴar shekara 5 da malamin makarantar su Noble Kids Academy, Abdulmalik Tanko, ta fusata ta nannaushe shi bayan da ƴan sanda su ka kawo shi Shalkwatar Ƴan Sanda a Kano.
Daily Nigerian Hausa ta rawaito cewa a ranar Laraba ne dai dubun Tanko ta cika, bayan da ya ɗauke Hanifah tsawon sama da kwanaki 40, inda da ga bisani ya kashe ta bayan ya karɓi wani abu daga cikin naira miliyan 6 da ya ce a bashi kuɗin fansa.
A yau Juma’a ne Rundunar Ƴan Sanda ta yi holon Tanko da sauran waɗanda ake zargi da hannu a kashe yarinyar.
Jaridar indaranka ta rawaito cewa su ma iyayen marigayiya Hanifah sun zo shelkwatar ƴan sandan.
Jaridar ta ce iyayen Hanifah ne su ka fara zuwa wajenz inda da ga bisani sai a ka kawo Tanko da sauran waɗanda a ke zargi.
Da ga zuwan masu laifin, sai mahaifiyar Hanifah, Fatima Maina, ta hango Tanko, in da ta yi kansa, ta cakumo shi, sannan ta riƙa zabga masa mari da naushi.
Lamarin ya sanya ƴan sanda su ka zaburar su ka ɗauke Tanko ɗin, inda saura kuma su ka riƙa baiwa Fatima haƙuri.
-
News5 days agoWasu Ƴan Daba Sun Kai Farmaki Kasuwar Siyar Da Wayoyi Ta Farm Center Dake Kano
-
News7 days agoWasu Fusatattun Matasa Sun Ƙona Mutum Uku Har lahira A Filato
-
News6 days agoAbin Takaici Ne A Kyale Mata Su Cire Wandunan Da Aka Basu Akan Titi Suna Dagawa A Cikin Al’ummar Da Ke Alfahari Da Kunya Da Addini
