Connect with us

News

Buhari zai samar da ingantantaccen tsaro sama da yadda ya ke kafin ya hau mulki — Minista

Published

on

FB IMG 16440454136046009
Spread the love

Daga yasir sani abdullahi

 

 

Advertisement

Ministan Harkokin Ƴan Sanda, Maigari Dingyadi ya ce Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari na fafutukar gyara harkar tsaro ya kuma inganta ta samma da yadda ta ke lokacin da ya hau mulki.

Dingyadi ya baiyana haka ne a yayin ƙaddamar da Kwamitin Wayar da kai da Karɓar Ƙorafe-ƙorafe na Yan Sanda, PPCC, na Arewa-Maso-Yamma a ranar Alhamis a Sokoto.

Ya ce ƙaddamar da kwamitin wani yunƙuri ne Gwamnatin Taraiya wajen ƙara inganta aiyukan ƴan sanda domin ƙarfafa aikin su bisa kan doka da kuma kare haƙƙin ɗan adam.

Advertisement

Ya yi nuni da cewa PPCC wani tsari ne da a ka ƙirkiro domin magance matsalar rashin jituwa tsakanin ƴan sanda da al’umma a yayin gudanar da aikin su.

Dingyadi ya ƙara da cewa kwamitin zai baiwa al’umma damar kai ƙarar cin zarafi da ga ƴan sanda domin ɗaukar mataki da kuma daƙile ta’adar.

“Hakan na cikin ƙudurin shugaban ƙasa na samun ingantantaccen tsaro da ci gaban ƙasa,” In ji Ministan.

Advertisement

Ya kuma tabbatar da ƙudurin Buhari na inganta harkokin tsaro domin samar da ƙasa mai cike da zaman lafiya da tsaro sama da yadda ya samu ƙasar a 2015.

Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *