News
Buhari zai samar da ingantantaccen tsaro sama da yadda ya ke kafin ya hau mulki — Minista
Daga yasir sani abdullahi
Ministan Harkokin Ƴan Sanda, Maigari Dingyadi ya ce Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari na fafutukar gyara harkar tsaro ya kuma inganta ta samma da yadda ta ke lokacin da ya hau mulki.
Dingyadi ya baiyana haka ne a yayin ƙaddamar da Kwamitin Wayar da kai da Karɓar Ƙorafe-ƙorafe na Yan Sanda, PPCC, na Arewa-Maso-Yamma a ranar Alhamis a Sokoto.
Ya ce ƙaddamar da kwamitin wani yunƙuri ne Gwamnatin Taraiya wajen ƙara inganta aiyukan ƴan sanda domin ƙarfafa aikin su bisa kan doka da kuma kare haƙƙin ɗan adam.
Ya yi nuni da cewa PPCC wani tsari ne da a ka ƙirkiro domin magance matsalar rashin jituwa tsakanin ƴan sanda da al’umma a yayin gudanar da aikin su.
Dingyadi ya ƙara da cewa kwamitin zai baiwa al’umma damar kai ƙarar cin zarafi da ga ƴan sanda domin ɗaukar mataki da kuma daƙile ta’adar.
“Hakan na cikin ƙudurin shugaban ƙasa na samun ingantantaccen tsaro da ci gaban ƙasa,” In ji Ministan.
Ya kuma tabbatar da ƙudurin Buhari na inganta harkokin tsaro domin samar da ƙasa mai cike da zaman lafiya da tsaro sama da yadda ya samu ƙasar a 2015.
-
News5 days agoWasu Ƴan Daba Sun Kai Farmaki Kasuwar Siyar Da Wayoyi Ta Farm Center Dake Kano
-
News7 days agoWasu Fusatattun Matasa Sun Ƙona Mutum Uku Har lahira A Filato
-
News6 days agoAbin Takaici Ne A Kyale Mata Su Cire Wandunan Da Aka Basu Akan Titi Suna Dagawa A Cikin Al’ummar Da Ke Alfahari Da Kunya Da Addini
