News
An Kama Mutum Da Kunamu 150 Boye A Tufafinsa A Filin Jirgin Sama
Hukumomi a Afirka ta Kudu sun kama wani mutum mai shekara 28 bayan an gano kunamu 150 rayayyu masu dafi, waɗanda aka ɓoye cikin tufafinsa a filin jiragen sama na ƙasa-da-ƙasa da ke Cape Town.
Hukumar ‘yansandan Afirka ta Kudu, (SAPS), ta ce an yi kamen ne ranar 12 ga Yuni a wani aiki da ɓangaren da ke yaƙi da safarar dabbobin masu fuskantar barazanar ƙarewa ya yi, bisa bayanan sirri da haɗin-gwiwar hukumar CapeNature mai kula da dabbobin daji.
Gwamnatin Kano Ta Mayar da Hankali Kan Matasa Domin Ƙara Yawan Masu Rajistar Masu Katin Zaɓe
Jami’ai sun gano wanda ake zargin ne ta hanyar amfani da kwatancen da aka ba su game da shi, kafin su kama shi su kuma bincika jakunkunansa.
Yayin binciken, hukumomi sun gano kunamu 150 masu dafi da ransu da ya ɓoye cikin tufafinsa. An kama wanda ake zargin bisa laifin riƙe namun daji ba bisa ƙa’ida ba, lamarin da ya saɓa wa dokokin kare halittu da muhalli.
-
News5 days ago
ICPC Ta Yi Barazanar Daurin Shekaru 7 Ga Masu Yiwa Baki Rajistar NIN A Matsayin Yan Najeriya
-
News1 day ago
Jam’iyyar ADC Ta Yi Watsi Da Cire Ta Daga Rijista, Ta Sha Alwashin Kalubalantar Hukuncin Kotu
-
News6 days ago
Hayar Jirage Hadi Sirika Ya Dakko Daga Habasha Don Damfarar Yan Najeriya Da Sunan “Nigeria Air” — Shaida
