Connect with us

News

An Kama Mutum Da Kunamu 150 Boye A Tufafinsa A Filin Jirgin Sama

Published

on

IMG 20260617 002939 350

Hukumomi a Afirka ta Kudu sun kama wani mutum mai shekara 28 bayan an gano kunamu 150 rayayyu masu dafi, waɗanda aka ɓoye cikin tufafinsa a filin jiragen sama na ƙasa-da-ƙasa da ke Cape Town.

Hukumar ‘yansandan Afirka ta Kudu, (SAPS), ta ce an yi kamen ne ranar 12 ga Yuni a wani aiki da ɓangaren da ke yaƙi da safarar dabbobin masu fuskantar barazanar ƙarewa ya yi, bisa bayanan sirri da haɗin-gwiwar hukumar CapeNature mai kula da dabbobin daji.

Advertisement

Gwamnatin Kano Ta Mayar da Hankali Kan Matasa Domin Ƙara Yawan Masu Rajistar Masu Katin Zaɓe

Jami’ai sun gano wanda ake zargin ne ta hanyar amfani da kwatancen da aka ba su game da shi, kafin su kama shi su kuma bincika jakunkunansa.

Advertisement

Yayin binciken, hukumomi sun gano kunamu 150 masu dafi da ransu da ya ɓoye cikin tufafinsa. An kama wanda ake zargin bisa laifin riƙe namun daji ba bisa ƙa’ida ba, lamarin da ya saɓa wa dokokin kare halittu da muhalli.

 

Advertisement

 

TRT AFRIKA 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending