News
Gwamnatin Kano Ta Mayar da Hankali Kan Matasa Domin Ƙara Yawan Masu Rajistar Masu Katin Zaɓe
Gwamnatin Kano Ta Mayar da Hankali Kan Matasa Domin Ƙara Yawan Masu Rajistar Masu Katin Zaɓekan jama’a da ƙarfafa masu cancantar kaɗa ƙuri’a su yi rajistar zaɓe, yayin da wa’adin kammala Rajistar Zaɓe ta Dindindin (CVR) da Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) ta sanya ya rage ƙasa da makonni biyar.
Shugaban Kwamitin Wayar da Kai Kan Rajistar Zaɓe ta Dindindin a Kano, Kwamared Ibrahim Abdullahi Wa’iya, ya ce an samar da dabaru da tsare-tsare na musamman domin tabbatar da ƙarin jama’a sun shiga aikin kafin ranar 10 ga watan Yuli da za a rufe rajistar.
Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Dakatar Da Hukuncin Soke Rajistar ADC Da Wasu Jam’iyyu
Wa’iya, wanda kuma shi ne Kwamishinan Yaɗa Labarai da Harkokin Cikin Gida na jihar, ya bayyana haka ne yayin ziyarar sa ido da ya kai wasu cibiyoyin rajistar zaɓe a jihar.
Ya ce Kano na ci gaba da kasancewa a sahun gaba a ƙasar nan wajen yawan masu yin rajistar zaɓe, lamarin da ya bayyana a matsayin shaida ta yadda al’ummar jihar ke nuna kishin ƙasa da kuma fahimtar muhimmancin shiga harkokin dimokuraɗiyya.
Ya kuma yabawa INEC kan tsarin tura ma’aikatan rajista zuwa sassa daban-daban na jihar domin kusantar da aikin ga jama’a, musamman a yankunan karkara da cibiyoyin ilimi.
A cewarsa, yadda ake gudanar da aikin a Jami’ar North West Kano, Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Aliko Dangote da ke Wudil da kuma Kwalejin Ilimi ta Tarayya da ke Bichi ya nuna kyakkyawan tsari da inganci.
“Ɗaukar cibiyoyin rajista zuwa manyan makarantu ya ƙara bai wa matasa da masu rajista karo na farko damar shiga cikin aikin cikin sauƙi. Wannan mataki ne mai matuƙar muhimmanci wajen faɗaɗa sahun masu kaɗa ƙuri’a,” in ji shi.
Ya yi kira ga duk masu cancantar yin rajistar da ba su yi ba da su yi amfani da damar kafin wa’adin ya cika.
A nasa ɓangaren, Shugaban Ƙungiyar Manyan Ma’aikatan Jami’o’i (SSANU) reshen Jami’ar North West Kano, Kwamared Muhammad Jaji, ya ce sun wayar da kan mambobinsu tare da ƙarfafa su su shiga aikin rajistar.
Haka kuma, Shugaban Ƙungiyar Ma’aikatan da Ba Na Koyarwa Ba (NASU) na jami’ar, Kwamared Bashir Muhammad, ya bayyana rajistar zaɓe a matsayin wani muhimmin nauyi na ɗan ƙasa da ke taimakawa wajen ƙarfafa dimokuraɗiyya.
Shi ma Shugaban Ƙungiyar Malaman Kwalejojin Ilimi (COEASU) a Kwalejin Ilimi ta Tarayya da ke Bichi, Dakta Ali Abubakar Ali, ya ce aikin zai ba ɗalibai da ma’aikatan makarantar damar taka rawar gani a zaɓuɓɓukan da ke shafar makomar ƙasa.
Ya yabawa jami’an INEC bisa ƙwarewa da nuna gaskiya wajen gudanar da aikin, tare da kira ga waɗanda har yanzu ba su yi rajista ba da su gaggauta yin hakan.
Yayin da wa’adin rufe rajistar ke ƙara matsowa, gwamnati da sauran masu ruwa da tsaki na ci gaba da ƙarfafa gangamin wayar da kai domin tabbatar da cewa duk masu cancantar kaɗa ƙuri’a a Kano sun samu damar yin rajista kafin ranar 10 ga Yuli.
