News
Tsaftar Muhalli: Gwamnatin Kano ta ci tarar kasuwar ƴankaba
Daga kabiru basiru fulatan
Kotun Tafi-da-gidanka da ta tare da Kwamitin Kar-ta-kwana a kan Tsaftar Muhalli na Jihar Kano ta ci tarar kasuwar ƴankaba Naira dubu 200.
Kotun ta ci tarar kasuwar ne sakamakon ƙin bin dokar tsaftar muhalli ta jihar.
Da ya ke yanke hukunci, Majistare Auwal Yusuf Suleman ya ce an kama kasuwar ne da laifin buɗe wa a cikin awannin hana fita waje sabo da tsaftar muhalli da a ka yi a duk Asabar ɗin ƙarshen wata a jihar.
Wakilin shugaban ƙungiyar ƴan kasuwar, Umar Ibrahim ya riƙe kotun da ta yi musu sassauci bayan ya amsa laifin buɗe kasuwar a lokacin da doka ta hana.
A nashi ɓangaren, Shugaban kwamitin, kuma Kwamishinan Muhalli na jihar, Dakta Kabiru Ibrahim Getso, wanda ya samu wakilci Babban Sakataren ma’aikatar, Adamu Abdu Faragai ya yi kira ga al’umma da su riƙa bin doka.
Ya kuma yaba wa kwamitin a bisa jajircewa wajen aikin sa da kuma tabbatar da an bi doka da oda.
-
News4 days ago
Ban Taɓa Nadamar Adawa Da Yunƙurin Obasanjo Na Wa’adin Mulki Karo Na Uku Ba — Atiku
-
News4 days ago
Jami’an Ƴansanda Sun Ƙwato Na’urorin Solar 160 Da Darajarsu Ta Kai Kimanin Naira 59.2 A Kano
-
News1 day ago
Wasu Kansiloli Na Zargin Ciyaman Da Daukar ‘Yan Daba Domin Kai Musu Hari A Kano
