Connect with us

News

Bom’ Ya Kashe Mutum 1, Wasu 7 Sun Jikkata A Gidan Giya A Yobe

Published

on

Daga yasir sani abdullahi

 

 

Mutum daya ya rasu, wasu akalla bakwai kuma sun jikkata sakamakon fashewar wani abu a wani gidan giya a Jihar Yobe.

Bayan Sallar Tarawi ne dai aka ji karar fashewar wani abu da ake tunanin bom ne a garin Gashua da ke Karamar Hukumar Bade a jihar ta Yobe.

An ci tarar bazawara N55,000 saboda zuwa kabarin mijinta da kare
Za a kwaso ’yan gudun hijirar Sakkwato 50,000 daga Nijar
Hakan ya yi sanadiyar mutuwar mutum daya wasu bakwai suka ji raunuka da kuma karaya.

Advertisement

Sai dai kuma wasu mazauna garin sun bayyana cewa tukunyar gas ce ta fashe a gidan wata amarya, ba bom ba.

Faruwar lamarin dai ya jawo hankalin Shugaban Karaman Hukumar ta Bade, Sanda Kara Bade, ziyartar wajen da abin ya faru tare da jami’an tsaro don gane wa kansa.

Shugaban ya dauki nauyin jinyar wadanda suka samu raunukan, wanda ya rasu kuma an kai gawarsa asibiti.

Nan take shugaban karamar hukumar ya kafa kwamitin gaggawa domin binciko hakikanin abin da ya faru sannan ya ba da umarni a rufe mashayan da ke garin na Gashua

Cikakken bayanin zai biyo baya.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending