Connect with us

News

YAN BINDIGA SUN KASHE MUTUM 8, SUN GINDAYA SHARADIN ZAMAN LAFIYA A JIHAR SAKKWATO.

Published

on

Daga Khadija Abdullahi Mahmud.

 

Advertisement

Wasu yan bindiga a jerin gwanon Mashina sun farmaki ƙauyen Taka Lime, da ke ƙaramar hukumar Goronyo a jihar Sokoto, inda suka kashe aƙalla mutum 8.

Jaridar Vanguard ta ruwaito cewa maharan sun tattara mutane da dama sun yi awon gaba da su, kuma sun sanar da mutanen kauyen abun da zai sa su zauna lafiya.

Advertisement

Wani mazaunin ƙauyen Taka Lime wanda ya rasa matarsa da ɗiyarsa a harin, Sani Takakume, ya ce yan ta’addan sun shigo kuma suka buɗe wuta kan mai uwa da wabi.

Ya ce:

Advertisement

“Mun fito da yawa ɗauke da dukkan wani nau’in makami domin mu kare kan mu daga maharan kuma muka ci nasarar kashe mutum uku, muka kama ɗaya.”
“Da suka fahimci mutanen kauye sun kashe musu mayaƙa uku, sai suka kashe mutum 8 daga cikin yan uwan mu da suke tsare da su da nufin ɗaukar fansa.”
Wane sharaɗi suka gindaya na zaman lafiya?
A cewarsa tuni yan bindigan suka bukaci a tattara musu zunzurutun kuɗi naira miliyan N10m a matsayin na fansar mutanen kauye da suka yi garkuwa da su.

Hakanan kuma sun gindaya sharaɗin cewa matukar mutane na son zaman lafiya a yankunan, dole su biya harajin miliyan N10m.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending