Connect with us

News

Hajjin bana: Gwamnatin Legas za ta mayar wa maniyyatan da basu samu kujera ba kuɗaɗensu

Published

on

Daga Maryam bashir musa 

 

Advertisement

Gwamnatin jihar Legas ta ce za ta mayar wa da maniyyata aikin Hajji kuɗaɗen su da suka biya amma basu samu kujera ba a Hajjin bana.

An kai masu gadi kotu bisa zargin satar ‘cornflakes’

Advertisement

Kwamishinan harkokin cikin gida, Prince Anofiu Elegushi, ne ya bayyana hakan a jiya Talata yayin wani taron manema labarai a cibiyar ‘yan jarida ta Bagauda Kaltho da ke Alausa, Ikeja.

 

Advertisement

Elegushi ya ce za a mayar wa da waɗanda abin ya shafa kuɗaɗen su cikakku, inda ya ƙara da cewa za a yi biyan cikin tsari da kuma gaggawa.

 

Advertisement

Ya ce gwamnatin jihar Legas za ta buga sunayen maniyyatan da abin ya shafa a a jaridun ƙasa a matsayin rukunin farko na aikin Hajjin 2023.

 

Advertisement

A cewarsa, gwamnati za ta kuma dakatar da sayar da fom na aikin Hajjin 2023, har zuwa lokacin da za a tabbatar da ainihin adadin kujerun da za a bayar.

 

Advertisement

Kwamishinan ya tabbatar wa dukkan maniyyatan jihar goyon bayan gwamnatin jihar a kowane lokaci tare da addu’ar Allah ya dawo da alhazan da aka riga aka yi jigilarsu gida lafiya.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending