News
Yan Bindiga Sun Fara Harbin Fasinjojin Jirgin Kasan Da Ke Hannunsu
’Daga Maryam bashir musa
’Yan bindigar da suka yi garkuwa da fasinjojin jirgin kasan Kaduna zuwa Abuja sun harbi daya daga cikin fasinjoijn da suka rage a hannunsu.
Hajjin bana: Gwamnatin Legas za ta mayar wa maniyyatan da basu samu kujera ba kuɗaɗensu
Daya daga cikin masu shiga tsakani domin a sako fasinjojin, Malam Tukur Mamu, wanda ya sa baki aka sako 11 daga cikin fasinjojin, ya ce mutumin da aka harba din yana cikin mawuyacin hali bayan harbin da suka yi mishi.
“Ina tabbatar muku da cewa an harbi fasinjan kuma majiya mai tushe ce ta sanar da ni hakan. Za ta iya yiwuwa da gangan suka harbe shi a matsayin wani sako.
“Kashe mutanen da ke hannunsu abu ne da muka san za su iya tunda a baya sun yi barazanar aikatawa,” inji shi.
Ya ce ya zama wajibi gwamnati ta dauki mataki a kan kari, idan ba haka ba ta shirya daukar alhakin duk abin da ya samu mutanen da ke hannun ’yan bindigar.
Ya bayyana cewa gwamnati na tattaunawa da maharan a-kai-a-kai, amma har yanzu ba ta yi wani kwakkwaran motsi ba.
“Na san abin da ke cikin wannan matsala shi ya sana nake nanata cewa ya kamata Shugaba Buhari ya dauki wasu matakai, marasa dadi, matukar za su kai ga kubutar da rayukan mutanen da ba su ji ba, ba su gani ba.”
Source Aminiya
