Connect with us

News

Yan Bindiga Sun Fara Harbin Fasinjojin Jirgin Kasan Da Ke Hannunsu

Published

on

 

Daga Maryam bashir musa 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

’Yan bindigar da suka yi garkuwa da fasinjojin jirgin kasan Kaduna zuwa Abuja sun harbi daya daga cikin fasinjoijn da suka rage a hannunsu.

Advertisement

Hajjin bana: Gwamnatin Legas za ta mayar wa maniyyatan da basu samu kujera ba kuɗaɗensu

Daya daga cikin masu shiga tsakani domin a sako fasinjojin, Malam Tukur Mamu, wanda ya sa baki aka sako 11 daga cikin fasinjojin, ya ce mutumin da aka harba din yana cikin mawuyacin hali bayan harbin da suka yi mishi.

Advertisement

 

 

Advertisement

 

“Ina tabbatar muku da cewa an harbi fasinjan kuma majiya mai tushe ce ta sanar da ni hakan. Za ta iya yiwuwa da gangan suka harbe shi a matsayin wani sako.

Advertisement

“Kashe mutanen da ke hannunsu abu ne da muka san za su iya tunda a baya sun yi barazanar aikatawa,” inji shi.

 

Advertisement

Ya ce ya zama wajibi gwamnati ta dauki mataki a kan kari, idan ba haka ba ta shirya daukar alhakin duk abin da ya samu mutanen da ke hannun ’yan bindigar.

Ya bayyana cewa gwamnati na tattaunawa da maharan a-kai-a-kai, amma har yanzu ba ta yi wani kwakkwaran motsi ba.

Advertisement

 

“Na san abin da ke cikin wannan matsala shi ya sana nake nanata cewa ya kamata Shugaba Buhari ya dauki wasu matakai, marasa dadi, matukar za su kai ga kubutar da rayukan mutanen da ba su ji ba, ba su gani ba.”

Advertisement

 

Source Aminiya 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending