Connect with us

News

Kano ta fi kowacce jiha yawan karɓar katin zaɓe — INEC

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Jihar Kano ce a kan gaba wajen yawan karɓar katin zaɓe a faɗin ƙasar nan, in ji Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa, INEC.

Advertisement

 

Jami’in hulɗa da jama’a na INEC, reshen Jihar Kano Adam Ahmad Maulud ne ya bayyana haka a lokacin da ya ke zantawa da manema labarai a yau Laraba a Kano.

Advertisement

Ranar Alhamis Masu Gidajen Burodin Najeriya Za Su Fara Yajin Aiki

Ya ce ofishin INEC na kano ya buɗe sabuwar cibiyar rajista a filin wasa na Sani Abacha, inda ya ce akwaina’urorin yin rijistar sama da guda 30 a wajen.

Advertisement

 

Maulud ya bayyana cewa sabuwar cibiyar tana aiki sau uku a mako, wato ranekun Talata, Laraba, da Alhamis.

Advertisement

 

“A wata sanarwa da ta gabata, jihar Kano ce ta zo ta biyu wajen yin rijistar, amma na yi imani da wannan fitowar da mutane sukai wajen karbar katin zaben, muna kan gaban dukkan jihohin kasar nan.”

Advertisement

 

Jami’in hulda da jama’ar ya kara da cewa, ɗimbin jama’ar da suka fito domin sake tantance yin katin zabe ya biyo bayan gagarumin gangamin wayar da kan jama’a ne da INEC ta yi kan mahimmancin rajistar.

Advertisement

 

Idan dai za a iya tunawa INEC ta sanya ranar 30 ga watan Yuli a matsayin wa’adin ranar rufe aikin rajistar.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending