Connect with us

Entertainment

Manhajar kallon fina-finai ta yanar gizo, kallo.ng ta samu lambar girma a Ghana

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Watanni takwas kacal da ƙaddamar da manhajar kallon fina-finan Hausa ta yanar gizo, mai suna kallo.ng, ta samu lambar girma a Ghana.

 

Advertisement

Kallo.ng ta samu lambar girman ne daga Marketing World Award, MWA, kamfanin da yayi shura wajen bada lambar girma ga wadanda su ka yi bajinta a harkar finafinai.

Ƴan fashin daji na ta kwararowa jiha ta, Gwamnan Nassarawa ya koka

Advertisement

 

An bada lambar girman ne a ranar 15 ga watan Yuli, a wani katafaren taro da s ka yi a birnin Accra na ƙasar Ghana.

Advertisement

 

A wata sanarwa da ta fitar a Kano a jiya Asabar, shugabar kallo.ng, Hajiya Maijidda Moddibo, ta bayyana cewa lambar girman wata gagarumar nasara ce.

Advertisement

 

A cewar ta, kamfanin ma kallo.ng ya samu nasarar ne duba da irin jajircewarsa wajen ganin ya inganta manhajar, wajen amfani da sabbin fasahohin zamani, don biyan buƙatar abokan hulɗarsa.

Advertisement

 

Maijidda ta kuma ƙara da cewa kamfanin kallo.ng ya tsaya kai da fata don ganin ya mayar da manhajar ta zama daidai da tsarin tafiyar da manhajar kallon fina-finai na duniya.

Advertisement

 

Ta kuma bayyana cewa yanzu haka kamfanin na kallo.ng, duba da irin dabarun zamani da ya ke bullowa da su, ya samu sama da mutane dubu 35 da su ka kulla alaƙa da shi.

Advertisement

 

Ta kuma ci alwashin ci gaba da inganta ayyukan kamfanin don biyan buƙatar abokan hulɗa.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending