Politics
Simon Baƙo Lalong Ya zama shugaban yakin Neman zaben tinubu
Daga Yasir sani Abdullahi
Jam’iyyar APC ta naɗa Gwamnan jihar Plateau Simon Baƙo Lalong a matsayin sabon shugaban yaƙin neman zaben ɗan takarar shugabancin ƙasa Asiwaju Bola Ahmad Tinubu a kakar zaben 2023.
Jaridar siyasar mu ta rawaito Shugaban jam,iyyar APC na ƙasa, Sanata Abdullahi Adamu shine ya bayyana hakan lokacin da yake zantawa da manema labarai a fadar Villa, bayan ya kammala tattaunawa da shugaban kasar Nigeria muhammadu buhari
Kuma ya bayyana festus keyamo a matsayin shine Mai magana da yawun shugaban yakin Neman zaben sai Kuma hannatu Musa a matsayin mataimakiya
Advertisements
