Connect with us

News

Yan Sanda Sun Kama Sojoji 2 Da Zargin Hallaka Sheik Aisami

Published

on

Daga Muhammad Muhammad zahraddin

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Rundunar ‘yan sandan jihar Yobe ta kama wasu sojoji biyu da ake zargi da kashe wani shahararren malamin addinin Islama, Sheikh Goni Aisami da aka kashe a ranar Juma’a da misalin karfe 9 na dare.

Advertisement

Jaridar INDARANKA ta rawaito cewa an Harbe malamin ne a kan hanyarsa ta zuwa Gashua daga Kano.

Wasu majiyoyin sirri da dama sun yi zargin cewa sojoji sun kashe malamin ne bayan da ya rage musu hanya daga shingayen binciken sojoji na Nguru zuwa Jaji-maji, da ke kusa da karamar hukumar Karasuwa a jihar Yobe.

Advertisement

Majiyar ta ce an harbe shi ne sanda suke tafiya, kuma daga bisani sojojin suke tsere da motar sa kirar Honda Accord, kafin daga bisani ‘yan sanda su kama su.

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Yobe, Dungus Abdulkarim, ya ce sojojin biyu da aka kama su ne Lance Kofur John Gabriel da Lance Kofur Adamu Gideon na 241 Recce Battalion, Nguru, jihar Yobe.

Advertisement

Ya ce an kai mutanen biyu zuwa sashin binciken manyan laifuka na rundunar da ke Damaturu domin gudanar da bincike.

An yi jana’izar fitaccen malamin nan ne a ranar Asabar a garin Gashua da ke Jihar Yobe a yayin da dubban dalibansa da ‘yan uwa da abokan arziki suke ta jimamin mutuwarsa.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending