Connect with us

News

Abin Kunya Ne A Ce Har Yanzu Najeriya Na Shigo Da Man Fetur

Published

on

Godwin Obaseki, Gwamnan Jihar Edo

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Gwamnan jihar Edo, Godwin Obaseki, ya ce abin kunya ne Najeriya ta ci gaba da shigo da albarkatun man fetur daga ketare duk da kasancewarta daya daga cikin manyan masu samar da shi a duniya.

Advertisement

 

Ya bayyana hakan ne ranar Lahadi a garin Ewohimi da ke karamar hukumar Esan ta Kudu maso Gabas da ke jihar, yayin taron shekara 10 da tunawa da Cif Jeremiah Ighodalo, mahaifin shugaban bankin Sterling, Dokta Asue Ighodalo.

Advertisement

Wace ce Liz Truss? – sabuwar Firaministar Birtaniya

Gwamnan ya ce, “Ci gaba da shigo da mai Najeriya babban abin kunya ne ga kasar.

Advertisement

 

“A matsayinta na ja-gaba wajen samar da danyen man a nahiyar Afirka, bai cancanci a ce Najeriya na shigo da mai daga waje ba. Gaskiya abin kunya ne a ce har yanzu muna shigo da shi.

Advertisement

 

“A matsayinmu na kasa a daidai wannan lokacin abin kunya ne babba ci gaba da shigo da man,” inji Gwamna Obaseki.

Advertisement

 

Shi ma da yake nasa jawabin kan matatar man da yake ginawa, shugaban rukunin kamfanonin Dangote, Alhaji Aliko Dangote, ya ce yana fatan a cikin shekarar 2023 za ta fara aiki gadan-gadan.

Advertisement

 

Ya ce matatar za ta samar da man da ilahirin Najeriya da ma makwabtan kasashe za su rika amfani da shi.

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

DAILY TRUST

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending