News
Sabon Ginin Beni Da Ake Ginawa Shima Ya Fara Rikitowa A Kano
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Wani sabon ginin beni mai hawa biyu a kasuwar ƙofar Wambai cikin filin idi dake birnin Kano ya fara ruguzowa, kamar yadda JARIDAR ALKIBLAH ta rawaito.
Da safiyar ranar Alhamis ne dai ginin ya fara rusowa a lokacin da masu aikin suka je domin ci gaba da yin aikin ginin.
Mali ta gargadi ECOWAS kan tsoma baki game da batun sojojin Ivory Coast da ke hannuta
Wasu da suke gudanar da sana’o’in su a daf da wajen sun bayyanawa jaridar indaranka cewa tun farkon fara wannan ginin bene akwai rashin ƙwarewa da tsari daga masu gudanar aikin.
Usman Mohammed na ɗaya daga cikin masu kasuwanci a kasuwar ƙofar Wambai filin Idi ya ce.
“Tun farko da aka faro wannan gini babu tsari, domin tun da aka fara muke tofa albarkacin bakin mu bisa yanda aka ɗauko shi babu Injiniya wanda zai tsara wajan.”
Mohammed ya ƙara da cewa “Tunda aka fara aikin yau sai a fasa nan, gobe kuma a yaɓe can. a haka aka ɗauko ginin har zuwa yanzu.”
“Dan Ni kaina a kullum idan na tashi hankali na baya kwanciya, saboda tsoro na ke kada ginin ya faɗo domin na ga abinda ya faru a maƙotan kasuwannin mu.”
Shima wani mai sana’ar POS a daf da wajan Ahmad Abdullahi Muhammad ya bayyana cewa, lokacin da lamarin ya faru suna kan zuba Dakin ɗin Kankare ne a sama ya fara faɗowa, domin a kan ido na aka yi.
“Amma dai yanayin ginin babu inganci tun daga hawa na farko da aka yi”
Wannan dai na zuwa ne yan makwannin kaɗan da ruguzowar wani ginin bene a kasuwar yan waya ta Beruit da ke a jihar ta Kano, Wanda ya yi sanadiyar mutuwar mutane 3 da kuma Jikkatar wasu da dama.
