News
Kotu ta soke zaben fidda gwanin gwamna a Zamfara
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Wata babbar kotun tarayya a jihar Zamfara ta soke zaben fidda gwanin da ya tsayar da Alhaji Dauda Lawal Dare a matsayin dan takarar gwamnan jihar a karkashin jam’iyyar PDP a zabe mai zuwa.
Wani tsohon dan majalisar tarayya, wanda kuma ya tsaya takara a zaben, Alhaji Ibrahim Shehu Gusau, ya garzaya kotu yana neman a soke zaben fidda gwani na jam’iyyar PDP da Dare ya lashe, saboda rashin bin ka’ida.
Najeriya da Morocco sun sanya hannu kan yarjejeniyar shimfida bututun iskar gas
Da yake yanke hukuncin a ranar Juma’a, Mai shari’a Aminu Baffa Aliyu ya ce kotun ta amince da dukkanin addu’o’in da mai kara ya yi. Hukuncin yana kunshe ne a cikin takarda mai shafuka 109.
Mai shari’a Aminu ya bayar da umarnin cewa dole ne a sake gudanar da sabon zaben fidda gwani domin tabbatar da adalci da adalci ga kowane bangare.
Da yake jawabi jim kadan bayan yanke hukuncin, lauyan wanda ya shigar da kara, Barista Ibrahim Ali, ya ce, “Kotu ta duba ingancin lamarin kuma ta yanke hukunci a kan wadanda suka shigar da kara.”
Ya kara da cewa, “Addu’armu ita ce, kotu ta soke zaben fidda gwani da kwamitin da Adamu Maina Waziri ya jagoranta, sannan kotu ta ba da umarnin a gudanar da sabon zabe kamar yadda kundin tsarin mulkin PDP da ka’idojinsa suka tanada. Dukkan addu’o’inmu an biya su.
“An yi la’akari da hukuncin da kyau saboda mun tabbatar da shari’ar mu ba tare da shakka ba kuma mun yi farin ciki da hukuncin da kotu ta yanke.”
Sai dai mashawarcin jam’iyyar PDP a jihar a fannin shari’a, Barista Bashir Abubakar Masama, ya ce jam’iyyar za ta yi nazari kan hukuncin da za ta dauka, inda ya ce za a daukaka kara kan hukuncin.
DAILY TRUST
