Connect with us

News

Yan sanda sun kama ɗan firamare kan zargin bai wa malama alewa mai guba

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

 

 

Advertisement

 

Ana zargin wani dalibin firamare dan shekara goma da yunkurin kashe malamarsa da wasu takwarorinsa dalibai 12 a garin Njimbam na yammacin Kamaru.

Advertisement

Rahotanni na cewa, malamar ta aiki dalibin ne don ya sayo mata alewa, amma sai aka yi zargin cewa an zuba guba a ciki.

Kotun Najeriya ta ba da umarnin a kamo wani dan Burtaniya

Advertisement

Malamar dai ta karbi alewar, inda ta sha sannan ta raba wa karin daliban ajinta.

Jim kadan da shan alewar ne, sai malama da daliban suka fara kukan ciwon ciki, kafin daga bisani ajin ya rude.

Advertisement

Tuni dai aka garzaya da marasa lafiyan zuwa asibiti, kuma zuwa yanzu babu rahoto na mutuwar wani a cikin wadanda suka sha alewar

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending