Connect with us

News

Ranar Malamai: Daliban Kano Na Neman A Inganta Walwalar Malamai

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Daliban sakandare a Jihar Kano sun bukaci gwamnati ta inganta bangaren walwalar malaman makaranta domin samun karsashin koyarwa da ingantaccen ilimi.

 

Advertisement

Daliban sun bayyana hakan ne a ganawarsu da Aminiya, a bikin Ranar Malamai ta Duniya da Hukumar Raya Ilimi da Kimiyya da Al’adu ta Majalisar Dinkin Duniya (UNESCO) ta ware kowace ranar biyar 5 ga watan Oktoba domin ta.

Gobara Ta Kashe Mutum 9, An Ceto 72 A Kano

Advertisement

 

Muhammad Mukhtar da ke karatunsa na Sakandare a Makarantar Tangaza da ke Kano, ya bayyana farin cikinsa da zuwan ranar, tare da rokon gwamnati ta duba bukatun malaman ta biya musu.

Advertisement

 

Ita ma wata daliba, Khadijah Nasir, ta ce malamai ne ruhin kowacce al’umma, don haka akwai bukatar kyautata wuraren da suke aiki, da kuma magance musu matsalolinsu.

Advertisement

 

Shi ma wani dalibi, Muhammad Bello, ya ce akwai bukatar girmama malamai duk inda suke.

Advertisement

 

“Akan samu wadanda ba sa girmama su, wasu kuma a yi dace idan sun girma su yi ta neman malaman nasu bisa mutuncin da suka yi musu lokacin da suke dalibai, domin su ma su kyautata musu,” in ji shi.

Advertisement

 

A karshe ya yi kira ga gwamnati da ta kara kaimi wajen inganta walwalar malaman, da biyan su hakkokinsu domin su ne ginshikin al’umma.

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending