Connect with us

News

Saba Dokokin Hanya: Kotu Ta Hukunta Mutum 35 A Edo

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

 

 

 

A kalla mutum 35 ne kotun tafi-da-gidanka ta hukunta a Jihar Edo a ranar Alhamis bayan da ta kama su da laifukan saba dokokin hanya.

Advertisement

 

Ajiye mota a kan hanya ba bisa ka’ida ba, sauke bafasinja a wuraren da aka haramta, rashin kiyaye ka’idojin tuki da sauransu, na daga cikin laifukan da aka aikata da kotun ta ce ba ta yarda da hakan ba.

 

 

Minista ya ba da hakuri saboda tsananin lalacewar tituna

 

Advertisement

Lauyan gwamnatin jihar, Mista Ayo Aigbokhiade, ya ce a kwaryar birnin Benin aka kama duka masu lafin.

 

Alkalin kotun, Mutairu Oare, ya ba da umarnin duka masu laifin kowannensu ya biya tarar N25,000 a cikin kwana biyu.

 

Sai dai alkalin ya ci daya daga cikinsu tarar N40,000 saboda daukar fasinja da ya yi a dandalin King’s Square.

 

Advertisement

An sallami wasu mutum biyu daga cikin wadanda aka gurfanar wa kotun saboda ba a same su da aikata kowane laifi ba.

 

 

 

 

 

Advertisement

DAILY TRUST

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending