Connect with us

News

Kotun Daukaka Kara ta Najeriya ta umarci ASUU ta koma aiki ba bata lokaci

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Kotun Daukaka kara ta Najeriya ta umarci kungiyar malaman jami’o’i ta kasar, ASUU da ta gaggauta komawa bakin aiki ba tare da bata wani lokaci ba.

 

Advertisement

Hukuncin ya biyo bayan daukaka karar da kungiyar ta yi ne a kan hukuncin da Kotun Kwadago ta kasar ta yi ne inda ta umarci kungiyar ta ASSU da ta kawo karshen yajin aikin da ta kwashe wata bakwai tana yi.

Bankin CBN Ya Bai Wa Masu Kananan Sana’o’i Tallafin Tiriliyan N2.1

Advertisement

Yayin yanke hukuncin kotun daukaka karar ta ce janye yajin aikin shi ne sharadin kawai da zai sa ta samu damar daukaka kara da ta yi kan hukuncin kotun kwadagon.

 

Advertisement

A kan hakan ne kotun ta yarda ta saurari daukaka karar amma da sharadin kungiyar ta janye yajin aikin da take yi ba tare da bata wani lokaci ba, kafin a kai ga warware ainahin shari’ar da ake yi kan batun.

 

Advertisement

Ita dai ASUU tana yajin aiki tun ranar 14 ga watan Fabrairu, inda mambobinta wato malaman jami’o’in gwamnati suka dakatar da aiki a kan kin biyansu kudaden alawus-alawus tare da neman kyautata jin dadinsu da sauran bukatu daga gwamnatin tarayya.

 

Advertisement

Gwamatin Najeriya ta yi wa wasu sabbin kungiyoyi biyu na malaman jami’a da suka bullo wadanda ke zaman tamkar kishiya ga ASUU.

 

Advertisement

Kungiyoyi su ne CONUA da NAMDA ( Congress of Nigerian Universities Academics) da (National Association of Medical and Dental Academics).

 

Advertisement

Kuma ASUU ta ce za ta kai gwamnati kara kan yi wa kungiyoyin biyu rijista.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending