Connect with us

News

Ɗalibin da ya koma sayar da abinci sabo da yajin aikin ASUU ya rasu

Published

on

Usman Rimi

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

 

 

 

 

Advertisement

 

 

 

Usman Rimi, ɗalibin da ke shekarar karshe a fannin likitanci da tiyata a Jami’ar Usmanu Danfodiyo Sokoto, UDUS, wanda ya tsunduma harkar sayar da abinci sakamakon yajin aikin ASUU, ya rasu.

 

Rimi ya bude shagon sayar da abinci da dafa Indomie a yankin Diplomat da ke Sokoto.

Advertisement

Kiwon Kaji: Yadda Aka Yi Wa Masu Neman Tallafi Damfarar N819m A Kano

Kamfanin Dillancin Labarai na Ƙasa, NAN ya bayar da rahoton cewa ɗalibin ya rasu ne a ranar Laraba bayan gajeriyar rashin lafiya.

 

Shugaban cibiyar ƴan kasuwa ta 21st Century Entrepreneur Hub, Umar Idris, na kusa da marigayin, shi ne ya tabbatar wa NAN rasuwar a yau Asabar.

 

Idris ya ce an yi jana’izar marigayin kamar yadda addinin Musulunci ya tanada a garinsu, Rimi da ke Ƙaramar Hukumar Rimi a jihar Katsina.

Advertisement

 

Ya bayyana marigayin a matsayin mutum mai tawali’u kuma dalibi mai kwazo kuma dan kasuwa.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending