Connect with us

News

Tsofaffin Fuskokin Da Ba Za Su Dawo Majalisar Tarayya Ba

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAH 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Jaridar Daily Trust ta rairayo jerin wasu ’yan Majalisar Tarayya 16 da ba za su koma zauren majalisar ba bayan Babban Zabe na shekarar 2023.

Advertisement

 

Kamar yadda dai masu iya magana ke cewa, wadannan ’yan majalisar sun ci ‘taliyar karshe’ a kujerunsu na wakilci.

Advertisement

 

A yayin da wasu daga cikinsu ba za su koma ba saboda sun tsaya takarar neman wasu mukaman siyasa daban-daban da suke yi, wasunsu kuma ba za su samu damar komawa ba ce saboda gaza kai bantensu a yayin zaben fid-da-gwanayen takara ne kujerumnsu.

Advertisement

 

Galibi, kadan ne daga cikinsu kuma suka yi watsi da neman maimaita mukamansu a Zauren Majalisar ta Kasa.

Advertisement

 

Daga cikin ’yan majalisar da za su yi bankwana da ita dai akwai Shugaban Majalisar Dattawa, Ahmad Lawan da Yakubu Dogara da Ike Ekweremadu da Oluremi Tinubu da kuma Smart Adeyemi.

Advertisement

 

Sanata Ahmad Ibrahim Lawan:

Advertisement

Yana daya daga cikin wadanda suka fi dadewa a zauren majalisa, kuma ya soma ne daga Majalisar Wakilai, inda aka zabe shi a shekarar 1999 ya wakilci mazabar Bade da Jakusko ta Jihar yobe.

 

Advertisement

An kuma sake zabar sa a 2003 inda ya maimaita wannan kujera.

 

Advertisement

Daga wannan kuma ya koma Majalisar Dattawa inda ya wakilci mazabar Yobe ta Arewa tun daga lokacin har zuwa yanzu.

 

Advertisement

Sai dai a yanzu ba zai sake komawa majalisar ba, idan wa’adinsa ya kare a 2023, sakamakon umarnin kotu da ta ba Bashir Machina takarar kujerar tana mai tabbatar da cewa Lawan din bai shiga takarar zaben fidda gwani.

 

Advertisement

Ike Ekweremadu (mazabar Enugu ta Yamma)

Sau uku yana zama Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, ya kuma shiga majalisar ne a shekara 2003 yana wakiltar mazabar Enugu ta Yamma.

Advertisement

 

Tun lokacin yake wakiltar wannan mazabar har tsawon shekara 20.

Advertisement

 

Ya dai sayi fom na tsayawa tsakarar Gwamnan Jihar Enugu, amma ya janye aniyarsa ta tsayawa sa’o’i kadan kafin a yi zaben fitar da gwani.

Advertisement

 

A halin yanzu dai Ekweremadu yana tsare a Ingila bisa zargin safarar sassan jikin dan Adam.

Advertisement

 

Yakubu Dogara

Advertisement

Shi ne tsohon Shugaban Majalisar Wakilai daga mazabar Bogoro/Dass/Tafawa Balewa ta Jihar Bauchi.

 

Advertisement

Ya zama Shugaban Majalisar ne daga 2015 zuwa 2019, kafin rike wannan mukami, ya shugabanci kwamitoci da yawa.

 

Advertisement

Ya zama dan majalisa ne a shekarar 2007, kuma yana zauren har yanzu.

 

Advertisement

Sai dai ya yanke shawara ba zai sake komawa ba a bisa ra’ayi na kashin kansa.

 

Advertisement

James Manager (Mazabar Delta ta Kudu)

Shekararsa 20 a zauren majalisar za ta zo karshen wannan karon. Ya rike mayan mukamai a kwamitoci daban-daban na majalisar har da na makamashi, da kuma na kula da yankin Neja Delta.

Advertisement

 

Ya tsaya takarar Gwamnan Delta a jam’iyyarsa ta PDP amma ya fadi a zaben fid-da-gwani.

Advertisement

 

Abdullahi Ibrahim Gobir (Mazabar Sakkwato ta Gabas)

Advertisement

Sanatan mai wakiltar Mazabar Sakkwato ta Gabas ya kuma rike mukamai na jagora a Majalisar Dattawa.

 

Advertisement

Sau uku yana zama Sanata, biyu a karkashin PDP, bayan ya sauya sheka zuwa APC ya sake komawa.

 

Advertisement

Sai dai a yanzu ba zai sake komawa majalisar ba kasancewar ya nemi takarar kujerar gwamnan Sakkwato amma ya sha kaye a hannun Ahmed Aliyu.

 

Advertisement

Ajayi Boroffice (Mazabar Ondo ta Arewa)

Shi ne Mataimakin jagora a Majalisa Dattawa kuma sau uku yana zaman sanata daga mazabar Ondo ta Arewa.

Advertisement

 

Ya nuna sha’awarsa ta tsayawa takarar Shugaban Kasa a Jam’iyyarsa ta APC, amma ya janye wa Ahmed Tinubu a zaben fitar da gwani.

Advertisement

 

Ba kamar sauran ba, Ajayi da kansa ya janye daga takarar neman komawa Majalisar Dattawa.

Advertisement

 

Aliyu Sabi Abdullahi (Mazabar Neja ta Arewa)

Advertisement

Shi ne Mataimakin mai Tsawatarwa na Majalisar Dattawa, ya kuma yi kokarin samun tikitin takarar kujerarsa a zaben mai zuwa amma bai yi nasara ba.

 

Advertisement

Sakamakon shan kaye da ya yi a hannun gwamna mai ci Abubakar Sani Bello wanda ke shirin tafiya Majalisar idan ya kammala wa’adin mulkinsa.

 

Advertisement

Oluremi Tinubu (Mazabar Legas ta Tsakiya)

Ita ce matar Bola Ahmed Tinubu, shekarar ta 12 a zauren Majalisar Dattawa.

Advertisement

 

Sanatar ba ta nemi ta sake komawa majalisa ba a zabe mai zuwa ba zai rasa nasaba da takarar Shugaban Kasa da mijinta Bola Tinubu ya tsaya ba.

Advertisement

 

Oluremi ta rike mukamin Shugabar Kwamitin Sadarwa a Majalisar.

Advertisement

 

Smart Adeyemi (Mazabar Kogi ta Yamma)

Advertisement

Tsohon Shugaban ’Yan Jarida na Kasa ne, yana kuma wakiltar mazabar Kogi ta Yamma a Majalisar Dattawa, inda ya kwashe shekara 12.

 

Advertisement

Sai dai ba zai sake komawa zauren majalisar ba sakamakon shan kaye da ya yi a zaben fitar da gwani na mazabarsa.

 

Advertisement

Ya dangana hakan ne ga yadda yake sukar wasu manufofin jam’iyyarsa ta APC a zauren majalisar, wanda hakan ta sa aka kayar da shi, a cewarsa.

 

Advertisement

Leo Ogar (Delta ta Kudu)

Dan Majalisar Tarayyar na jam’iyyar PDP shi ne mai wakiltar Isoko ta Arewa da ta Kudu da ke Jihar Delta.

Advertisement

 

An kuma sake zaben sa a shekarar 2007 da 2011 da 2015 da kuma 2011.

Advertisement

 

Shi ke rike da mukamin jagoran majalisar, sannan ya taba shugabancin kwamitoci daban-daban na majalisar.

Advertisement

 

Ba zai koma zauren majalisar ba ne domin bai sake neman takarar kujerar ba.

Advertisement

 

Toby Okechukwu (Enugu)

Advertisement

Shi ne Mataimakin Shugaban Marasa Rinjaye a Majalisar Wakilai, yana kuma wakiltar mazabar Riba/Awgu/Aninri/ ta Jihar Enugu a karkashin Jam’iyyar PDP.

 

Advertisement

Ba zai koma zauren majalisar ba, sakamakon kaye da ya sha a zaben fidda da gwani a hannun Anayo Onwuegbu.

 

Advertisement

Pat Asdu (Enugu)

Shi ne yake wakiltar mazabar Nsukka/ Igbo-Eze ta Kudu ta Jihar Enugu.

Advertisement

 

Karonsa hudu yana komawa zauren majalisar a karkashin Jam’iyyar PDP.

Advertisement

 

Sai dai wannan karon ba zai koma ba, sakamakon kaye da ya sha a hannun Bitalis Abba a zaben fid-da-gwani na jam’iyyar.

Advertisement

 

Asadu ya danganta kayen da sha ga adawar ’yan Karamar Hukumar Nsukka da ya fi sauran tsanani.

Advertisement

 

Ossai Nicholas Ossai (Delta)

Advertisement

Ossai yana wakiltar mazabar Ndokwa/Ukwuani ta Jihar Delta.

 

Advertisement

Dan majalisar ya rike shugabancin kwamitoci daban-daban na majalisar ciki har da kwamitin yarjejeniya da tsare-tsare da tarbar baki.

 

Advertisement

Sau uku yana lashe zabe zuwa zauren majalisar, sai dai wannan karon za a yi babu shi a zauren majalisar, sakamakon kaye da ya sha a hannun Nnamdi Ezechi yayin zaben fid-da-gwani.

 

Advertisement

Herman Hembe (Binuwai)

Hemebe shi yake wakiltar mazabar Tarayya ta Jechira a Jihar Binuwai wanda ta wunshi kanana hukumomin Konshisha da Vandeikya.

Advertisement

 

Shekararsa 12 a zauren majalisar, ya kuma yanke shawarar ba zai koma ba, sakamakon tsayawa takarar kujerar gwamna da ya yi a jihar a karkashin jam’iyyar Labour a zaben 2023.

Advertisement

 

Uzoma Nkem-Abonta (Abia)

Advertisement

Uzoma shi yake wakiltar Ukwa ta Gabas da ta Yamma ta Jihar Abia.

 

Advertisement

Ya kuma shiga zauren majalisar ne a shekarar 2007, a karkashin Jam’iyyar PDP.

 

Advertisement

Dan majalisar ya rike shugabancin kwamitin sauraron koke-koken jama’a.

 

Advertisement

Ba zai sake komawa zauren majalisar ba a wannan karon sakamakon shan kaye da ya yi a zaben fitar da gwani na jama’iyyarsa.

 

Advertisement

Umar Mohammed Bago (Neja)

Shi yake wakiltar mazabar Chanchaga ta Jihar Neja a Majalisar Wakilai.

Advertisement

 

Ya shiga zauren majalisar ne a shekarar 2011 kuma ake damawa da shi har yanzu.

Advertisement

 

Dan majalisar ya yi aiki a kwamitoci da yawa, cikin har da na yaki da cin hanci da rashawa, da na hulda da jama’a da yada labarai, da kuma na harkokin da suka shafi kudi da bankuna.

Advertisement

 

Ba zai koma zauren majalisar ba saboda ya tsaya takarar Gwamnan Jihar Neja a Jam’iyyar APC a zabe mai zuwa.

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending