News
INEC Ta Ja Kunnen Yan Takara da Jam’iyun Siyasa
DADA YASIR SANI ABDULLAHI
Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC ta nuna damuwarta game da arangamar da ake samu tsakanin magoya bayan jam’iyun siyasan dake adawa da juna, yayin yakin neman zabe a fadin kasar nan
2023: Jam’iyyun Kano Sun Ki Fara Kamfe, Mako 1 Bayan Kada Gangar Siyasa
Punch ta ruwaito cewa, Shugaban Hukumar Mahmood Yakubu ne ya bayyana hakan a jiya Talata yayin taron da hukumar ta shirya kan babban zaben shekarar 2023 mai zuwa.
Ya bayyana cewa arangamar da ake samu tsakanin Magoya bayan jam’iyun siyasa a wasu jihohi dake kasar nan yayin yakin neman zabe abun da muwane matuka.
Shugaban hukumar ta INEC ya kuma bayyana cewa, akwai rahotannin hana wasu jam’iyun siyasa ko yan takara yin amfani da kayayyakin gwamnati a wasu jihohin dake fadin kasar nan
Kazalika ya hori Yan Takara Jam’iyun siyasa da magoya bayan su da su mai da hankali kan abun da ke gaban su, tare da kaucewa kaiwa junan su hari.
