Connect with us

News

Ɗan Sanda, wanda ya ƙi karɓar cin-hancin dala dubu 200 ya samu ƙarin girma

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Hukumar kula da harkokin ƴan sanda, PSC, ta sanar da karin girma na musamman ga CSP Daniel Amah, wanda ya ki karɓar cin hancin dala dubu 200, zuwa mukamin mataimakin kwamishinan ƴan sanda, ACP.

Advertisement

 

Kakakin hukumar, Azuka Ogugua, ce ta bayyana hakan a wata sanarwa da ta fitar a jiya Juma’a, a Abuja.

Advertisement

Gobara ta kashe mutane 3 a jahar Kano

Ogugua ta ce hukumar ta PSC ta kuma ba dan sandan kudi naira miliyan ɗaya, a matsayin tukwici da kuma kwarin gwiwa kan kiyaye mutuncin ƴan aikin ɗan sanda.

 

Advertisement

Shugabar hukumar ta PSC, Mai shari’a Clara Ogunbiyi, mai ritaya ta kotun koli, ta ce Amah ya nuna mutunci da kyawawan halaye da a ka san ɗan sanda da shi.

 

Advertisement

Ogunbiyi ta ce wannan tukwicin da karin girma na musamman zai zama wani kwarin gwiwa ga dukkan jami’an ƴan sanda su ci gaba da yin abin da ya dace a ko da yaushe a aikin su.

 

Advertisement

 

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending