Connect with us

News

Malaman Jami’o’i Sun Fara Yajin Aiki A Birtaniya

Published

on

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN 

 

 

 

Dubban ma’aikatan gwamnati, ciki har da ma’aikatan gidan waya da malaman jami’o’i da na kananan makarantu da sauransu, sun tsunduma yajin aiki a Birtaniya da zummar neman karin albashi.

 

Advertisement

Yajin aikin da aka soma ranar Alhamis ya jefa yanayin aiki a kasar cikin mawuyacin halin.

 

An rantsar da Anwar Ibrahim a matsayin sabon Firaiministan Malaysia

Ma’aikatan na neman a yi musu karin albashin ne don ba su damar iya yin rayuwa daidai da tsadar rayuwar da kasar ke fuskanta.

 

Makamashin girki da kayan abinci na daga cikin abubuwan da farashinsu ya yi tashin gwauron zabo, lamarin da ’yan kasar ke kokawa a kai.

 

Advertisement

Malamam jami’o’i kimanin 70,000 ne suka tsunduma yajin aiki a wannan Alhamis din a kasar, matakin da ya shafi karatun dalibai kimanin miliyan 2.5, inji rahotanni.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending