News
Nijar ta ɗauki harami gabanin taron ƙasashen Afirka
Yanzu haka shirye-shiryen sun kankama na tarukan ƙungiyar Tarayyar Afirka da za su gudana daga gobe Juma’a.
Shuwagabanin ƙasa da na gwamnatocin Afrika da dama ne suka riga suka isa Yamai babban birnin ƙasar, cikinsu har da Shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari.
Jim kaɗan bayan isarsa kasar ta Nijar ta karrama shi yayin wasu bukukuwa biyu da aka yi a yau Alhamis.
Bayan ba shi lambar yabon, an saka wa wani titi a Yamai sunansa, sannan kuma aka ƙaddamar da wani littafi da aka fassara daga turancin Ingilishi zuwa na Faransanci game da mulkin Shugaba Buhari.
Advertisements
