Connect with us

News

Ghana za ta fara tura wa Birtaniya malaman jinya

Published

on

Kweku-Agyeman-Manu

 

DAGA MUHAMAD MUHAMAD ZAHRADDIN

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Gwamnatocin Ghana da Birtaniya za su sanya hannu kan wata yarjejeniyar tura malaman jinya daga Ghana zuwa Birtaniya, wani abu da zai sanya Ghana ta samu ƙarin kuɗaɗen shiga da suka kai fan 1,000 a kan kowace malamar jinya ɗaya.

Advertisement

 

Ministan lafiya na ƙasar, Kweku-Agyeman-Manu ya shaida wa majalisar dokokin Ghana cewar “muna gab da sanya hannu kan yarjejeniyar, ciki har da waɗanda karatunsu ya tsaya a (ƙaramin) satifiket, za su je su samu horo sannan su dawo gida bayan shekara uku.”

Advertisement

Kotu Ta Daure Mataimakiyar Shugaban Argentina

A 2020 ma Ghana ta tura malaman jinya 100 zuwa tsibirin Barbados domin tallafa wa ƙasar wadda ke fama da ƙarancin malaman lafiya.

 

Advertisement

A baya dai shugaban Ghana Nana Akufo-Addo ya ce ƙasar na da wadatattun malaman jinya, har ma da rara, amma tura su asibitocin gwamnati na da wahala.

 

Advertisement

Sai dai shugabar ƙungiyar malaman jinya da ungo-zoma ta Ghana, Perpetual Ofori-Ampofo ta shaida wa BBC cewa ƙasar na fuskantar ƙarancin malaman jinya da za su yi aiki a asibitocin ƙasar.

 

Advertisement

Ghana na da malaman jinya masu rajista kimanin 120,000, amma kashi 46% ba su da babbar takardar karatu.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending