Connect with us

News

Ƙimata za ta zube idan na sake tsayawa takara – Jonathan

Published

on

Goodluck Jonathan

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Tsohon shugaban Najeriya Goodluck Jonathan ya ce ba zai sake tsayawa takarar shugabancin ƙasa ba kasancewar tsayawar za ta zubar masa da ƙima.

 

Advertisement

A wata tattaunawa da aka yi da shi lokacin bukin ƙaddamar da wani littafi kan rayuwa tsohon limamin cocin fadar shugaban ƙasa, a ranar Talata, Jonathan ya ce ƙaddara ce kawai za ta sanya ya sake zama shugaban Najeriya.

An sako basaraken da aka yi garkuwa da shi a Ondo

Ya ce amma shi da kansa ba zai taɓa tunanin sake zuwa ya sayi fom sannan ya bi mutane yana roƙon su su zaɓe shi ba.

Advertisement

 

A baya dai an yi ta raɗe-raɗin cewar tsohon shugaban ƙasar zai sake tsayawa takara a zaɓen 2023.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending