News
Babu wanda ya isa ya zarge ni da azurta kaina ta haramtacciyar hanya, in ji Buhari
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Shugaba Muhammadu Buhari na Najeriya ya ce babu wanda zai yi masa barazana kan azurta kansa ta haramtacciyar hanya a lokacin da yake mulki, yana mai cewa babu inci guda na kaddara dana mallaka a ketare.
Shugaba Buhari ya shaida hakan ne a wani taron liyyafa da aka shirya masa a birnin Damaturu na Yobe inda yake ziyara.
Sannan shugaban ya ce yana alfahari ganin cewa ya yaki Boko Haram kuma ya ga karshensu abin da yake cewa ya dawo da ayyuka da harkoki a yankunan arewa maso gabashin Najeriya.
Buhari ya ce ya sauke nauyi da alkauran da ya dauwa ‘yan Najeriya lokacin rantsuwar kama aiki a 2015 na kawar da Boko Haram na daidaito a kasar.
Shugaban ya kuma shaida yada hadin-kai da ya samu daga kasashe makwabtan Najeriya suka taimaka wajen yaki da ta’addanci.
Tun a jiya Litinin Buhari ya ziyarci Yobe inda ake saran ya kaddamar da wasu manyan ayyukan gwamnan Jihar.
