Connect with us

Uncategorized

Na san ƙuncin da janye tallafin mai ya jefa ku – Tinubu

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN

 

Advertisement

Shugaban kasa  Bola Ahmed Tinubu ya buƙaci al’ummar ƙasar su ɗan ƙara sadaukarwa da kansu domin ceto ƙasar daga durƙushewa.

A cikin jawabinsa na tunawa da Ranar Dimokraɗiyya, shugaba Tinubu ya ce ya san cewa shawarar gwamnatin ƙasar ta janye tallafin man fetur, za ta haddasa ƙarin wahala ga talakawa.

Advertisement

Sai dai in ji shi, wannan shawara ce wadda dole ne sai an ɗauka ta domin ceto Najeriya daga durƙushewa da kuma ƙwato dukiyar ƙasar daga hannun wasu tsirarun mutane marasa kishi.

Advertisement

Tinubu ya bai wa ‘yan Najeriya tabbacin cewa haƙurinsu ba zai tafi a banza, la’akari da yarda da amanar da ‘yan ƙasar suka bai wa gwamnatinsa.

Shugaba Tinubu ya ce gwamnatin da yake jagoranta za ta biya ‘yan Najeriya da gagarumin ƙoƙari zuba kuɗi cikin harkokin sufuri da bunƙasa da kuma samar da wutar lantarki a kai a kai baya ga ƙoƙarin bunƙasa harkokin kula da lafiya da sauran kayan amfanin al’umma.

Advertisement

A cewarsa sabon shugaban, gwamnatinsa za ta yi hakan ne don inganta rayuwa ga miliyoyin ‘yan Najeriya.

Ya ce tsarin dimokraɗiyyar da tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa Moshood Abiola ya mutu yana gwagwarmayar tabbatarwa a Najereiya shi ne wanda zai fifita da kuma kyautata jin daɗin al’umma a kan muradin ƙashin kai na shugabanni.

Advertisement

Da kuma tsarin da mutanen da ake mulka za su iya cimma burin rayuwarsu kuma su samu farin ciki.

Bola Ahmed Tinubu a cikin jawabin nasa ya nunar cewa shekara 30 kenan cif tun lokacin da ‘yan Najeriya suka gudanar da zaɓen shugaban ƙasa a 1993 don komawa ga tsarin dimokraɗiyya daga mulkin sojoji ‘yan kama-karya.

Advertisement

Kafin wata dokar soja ta rusa zaɓen 12 ga watan Yuni da ya bai wa Cif Moshood Kashimawo Olawale Abiola na jam’iyyar SDP nasara.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending