Connect with us

News

Buhari bai hana Tinubu binciken jami’an gwamnatinsa ba

Published

on

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN

Tsohon shugaban Najeriya Muhammadu Buhari bai hana sabon shugaban ƙasar Bola Tinubu binciken jami’an gwamnatinsa ba.

Advertisement

Cikin wani saƙo da mai magana da yawun tsohon shugaban Malam Garba Shehu ya wallafa a shafinsa ta twitter ya ce, labaran da ke yawo a shafukan sada zumunta, waɗanda ke cewa Buharin ya nemi Tinubu da kada ya binciki jami’an gwamnatinsa, labarai ne na ƙanzon-kurege.

Babu sulhu tsakaninmu da ‘yan bindiga – Gwamnatin Zamfara

Advertisement

Gabanin babbar salla ne Bola Tinubu ya gana da Buhari a wata ziyara da ya kai gidansa da ke Landan lokacin wata ziyarar ta ƙashin ƙai da Tinubun ya kai Landan bayan taron harkokin kuɗi na duniya da ya halarta a birnin Paris.

To amma Mallam Garba Shehu ya ce a lokacin ziyarar Buhari da Tinubun ne kawai suka gana babu wani mutum a ɗakin da suka gana, dan haka babu wanda ya san me suka tattauna.

Advertisement

Sanarwar ta kuma ce Buhari ya zaɓi fita daga Najeriya ne saboda gudun tsoma wa sabuwar gwamnati baki a al’amuranta.

View more on twitter

”Da farko ya zaɓi ya zauna a gidansa da ke Daura domin samun hutu da nutsuwar da yake buƙata, to amma hakan bai samu ba, kasancewar a kullum, dare da rana, safe da yamma ɗimbin mutane ne ke ziyartarsa”, in ji Mallam Garba Shehu cikin saƙon da ya wallafa.

Advertisement

Ya ƙara da cewa tsohon shugaban ya tafi Landan ne domin samun hutun da yake buƙata, sannan kuma hakan zai bayar da dama ga sabuwar gwamnatin Tinubu ta gudanar da ayyukanta wajen cika alƙawuran da suka ɗaukar wa talakawan Najeriya.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending