News
Yan Najeriya Sun Yi Zanga-Zanga Saboda Zabtare Kudaden Mutane Da Bankuna Ke Yi
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Yan Najeriya sun fito tituna a wasu yankunan Lagas domin yin zanga-zanga a kan yawan cajin da bankuna ne yi
Wani bidiyo da aka wallafa a Instagram ya nuna masu zanga-zanga rike da kwalaye dauke da rubutu iri-iri da ke nuna gajiyawarsu kan cajin Wasu masu amfani da soshiyal midiya sun yi martani ga zanga-zangar, suna masu bayyana cewa irin haka ya faru da su
Kwamishin ilmi mai zurfi na jihar Dr Yusuf Ibrahim Kofar ya Kaddamar Shirin duba Marasa Lafiya
Yan Najeriya Sun Yi Zanga-Zanga Saboda Zabtare Kudaden Mutane Da Bankuna Ke Yi
Takardun na dauke da rubutu kamar; “Muna son a fayyace mana gaskiya game da kudinmu,” “ku daina cire mana kudi haka kawai,” kuma “ku ce baku yarda da cajin banki mai yawa ba” da dai sauransu.
Wani labarin kuma Kwamishin ilmi mai zurfi na jihar Dr Yusuf Ibrahim Kofar ya Kaddamar Shirin duba Marasa Lafiya
Gwamnan jahar Ondo, Rotimi Akeredolu ya dawo gida Najeriya bayan dogon hutun da ya dauka domin duba lafiyarsa a kasar Jamus.
Gwamnan ya bar Najeriya watanni ukku da suka gabata domin duba lafiyarsa a kasar ta Jamus.
Shugaban masu rinjaye a zauren majalisar dokokin jihar Ondo, Wole Ogunmolasuyi, wanda ya tabbatar da dawowar gwamnan ga wakilinmu, Ya ce a yanzu haka gwamnan yana gidansa dake birnin Badun.
Kazalika maid akin gwamnan, Uwargida Betty ta tabbatar da dawowar mai gidan nata a shafinta na X, inda ta wallafa hotonsa a cikin jirgin sama.
