Connect with us

News

Bayanai kan sayen ‘jirgin ruwan kasaita na Shugaban Kasa’ a kasafin Kasa na 2023

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI.

 

Advertisement

Fadar shugaban ƙasar ta yi ƙarin bayani kan abin da take nufi da sayen “jirgin ruwan kasaita na shugaban ƙasa” da za a yi a cikin ƙwarya-ƙwaryan ƙarin kasafin kuɗi na shekarar 2023 da ta gabatar wa Majalisar Dokoki.

Akwai buƙatar yin ƙarin bayani kan sayen “jirgin ruwan shugaban ƙasa” da aka saka a ƙarin kasafin kuɗin 2023 da aka kai wa majalisa, sakamakon ce-ce-ku-cen jama’a da hakan ya jawo,” in ji sanarwar da aka wallafa a shafin X na Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Advertisement

Babban Bankin Kasa CBN Ya Musanta Rahotannin Karancin Kudade A Bankuna

Batun sayen jirgin ruwan wanda a cikin kasafin da aka gabatar wa majalisa aka kira shi da “jirgin ruwan kasaita na shugaban ƙasa” ya yi matuƙar tayar da ƙura a Nijeriya.

 

Advertisement

Fadar shugaban ƙasar ta ce “da farko dai akwai buƙatar mu fayyace cewa gwamnatin Shugaba Tinubu tana girmama ra’ayoyin ƴan Nijeriya a kan dukkan al’amuran da suka shafi jama’a.”

 

Advertisement

Sanarwar fadar ta yi wasu bayanai huɗu a kan abin da sayen “jirgin ƙasaita na shugaban ƙasa” ke nufi, kamar haka:

 

Advertisement

1. Idan aka ce Jirgin Ruwan Ƙasaita na Shugaban Ƙasa ana nufin wani Jirgin Yaƙin Sojin Ruwa mai wasu kayayyakin tsaro na musamman saboda yin muhimman ayyuka, ba wai don amfanin Shugaban Ƙasar ba.

 

Advertisement

Ana kiransa Jirgin Ruwan Kasaita na Shugaban Kasa ne saboda muhimman abubuwan tsaro da yake ɗauke da su.

 

Advertisement

2. Rundunar Sojin Ruwa ce ta yi odar jirgin ruwan tun a lokacin gwamnatin da ta gabata. Shugaba Tinubu ya sha cewa gwamnatinsa za ta ɗora kan ayyukan da gwamnatin baya take yi na abubuwan da ya gada daga fannin kadarori har na ayyuka.

 

Advertisement

3. Buƙatar biyan kuɗin sayen jirgin ruwan kuwa na daga cikin abin da ofishin Babban Hafsan Rundunar Sojin Ruwa ya gabatar ne ga Ma’aikatar Tsaro. Jumullar abin da aka buƙata shi ne naira biliyan 200, amma Shugaban Ƙasa ya amince ne kawai da naira biliyan 62.

 

Advertisement

 

4. Shugaba Tinubu yana mayar da hankali a kan tabbatar da tsaron ƙasarmu da iyakokinta na ruwa. Gwamnatin Tarayya a ƙarƙashin jagorancinsa tana zuba jari sosai don bunƙasa tattalin arziki a fannin man fetur da isakar gas da tattalin arzikin teku.

Advertisement

 

 

Advertisement

Trt Word

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending