News
Yajin aikin ƙungiyoyin ƙwadago haramtacce ne – Gwamnatin tarraya
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN
Gwamnatin tarayya ta bayyana rashin jin dadin ta game da matakin da kungiyoyin kwadago na kasa NLC da TUC suka dauka na fara yajin aikin a fadin kasar, duk da umarnin da kotun ma’aikata ta bayar na kada su yi yajin aiki.
A cikin wata sanarwa da ta fitar, gwamnatin ta bayyana matakin a matsayin wata alama ta girman kai da ƙoƙarin shafa wa gwamnati kashin kaji.
Sanarwar wadda ta samu sa hannun mai taimaka wa shugaba Tinubu kan yaɗa labarai da tsare-tsare, Bayo Onanuga ta ce “yajin aikin fatali ne da umarnin kotu da tozarta ɓangaren shari’a.”
Ta ƙara da cewa “Bai kamata ƙungiyoyin biyu su hukunta ƙasar baki daya ba kan wani lamari na ƙashin kai da ya shafi shugaban ƙwadagon, Joe Ajaero, wanda aka kai wa hari a Owerri”
Gwamnati ta jaddada kudirinta na gudanar da bincike kan harin da aka kai wa shugaban ƙungiyar Ajaero, inda ta ce babban sufeton ‘yan sanda ya bayar da umarnin a gudanar da bincike, kuma an canja kwamishinan ‘yan sandan jihar Imo.
Gwamnatin ta kuma jaddada cewa, yajin aikin, wanda ya bijirewa umarnin kotu, na nuni da rashin mutunta bangaren shari’a, kuma ya saɓawa ka’idojin kungiyar kwadago a tarihi.
-
News5 days ago
ICPC Ta Yi Barazanar Daurin Shekaru 7 Ga Masu Yiwa Baki Rajistar NIN A Matsayin Yan Najeriya
-
News1 day ago
Jam’iyyar ADC Ta Yi Watsi Da Cire Ta Daga Rijista, Ta Sha Alwashin Kalubalantar Hukuncin Kotu
-
News6 days ago
Hayar Jirage Hadi Sirika Ya Dakko Daga Habasha Don Damfarar Yan Najeriya Da Sunan “Nigeria Air” — Shaida
