Connect with us

News

Matashi ya kashe kansa bayan ya yi asarar Naira miliyan 2.5 a cacar yanar gizo

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Wani mutum mai shekaru 31 ya kashe kansa a jihar Abia, a kudu maso gabashin Najeriya, bayan da aka ce ya yi asarar Naira miliyan 2.5 a cacar yanar gizo.

Advertisement

Mutumin mai suna Chukwuma Onoh, an ce ya ciyo bashin Naira miliyan 1.2 daga hannun abokansa inda ya hada da na sa Naira miliyan 1.3 don yin buga cacan amma bai ci ba.

Rundunar Ƴan Sanda Sun Kama Masu Satar Mota A Jihar  Jigawa

” Zaɓin da ya rage min shine kawai in kashe kaina domin ba zan iya muamula cikin jama’a ba bayan irin wannan abin kunya da ya same ni, sannan kuma ta ina zan samu kuɗin biyan bashin da na ci na buga wannan caca.” Wannan shine saƙon da muka gani wanda mutumin ya saka a WhatsApp.

Advertisement

 

Matashin ya rika rubuta wa a shafin sa ta Facebook cewa shi zai kashe kansa saboda ya gaji da rayuwar duniya sannan bai san ta inda zai fara neman kuɗi ya biya masu bashi ba.

Advertisement

 

Ko da ya je siyan maganin kashe kwari ‘Sniper’ sai da ya rubuta a Facebook cewa ” Ga ni nan zan siya maganin kashe kwari zan sha in koma ga mahalicci na. Ba zan iya jure wa wannan hasara da na yi ba.

Advertisement

Ko da abokanan sa suka yi kokarin cimma sa, sun iske ya kwankwaɗi ruwan maganin har ya fara shureshure.

Premium Times ta ruwaito cewa Likitoci a asibiti sun tabbatar da ya sheka lahira, a lokacin da suke kokarin ceto sa.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending