Connect with us

Politics

Zaben Shugabannin Kananan Hukumomi: Jamiyyar NNPP Ta Baiwa Al’ummar Kano Tabbacin Gudanar Da Sahihin Zabe

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI

 

Advertisement

Jam’iyyar NNPP a jihar Kano ta baiwa al’ummar jihar tabbacin gudanar da sahihin zaben shugabannin kananan hukumomi da za a yi acikin wannan shekarar a jihar.

Shugaban jam’iyyar, Alhaji Hashimu Dungurawa ne ya bayar da wannan tabbacin lokacin da yake zantawa da manema labarai a Kano ranar Talata.

Advertisement

Yanzu-yanzu: Wani Abu Ya Fashe A Tashar Iskar Gas A Ibadan

Dungurawa ya ce “A matsayin jam’iyyarmu ta dimokuradiyya wacce manufofinta suka kasance don muradun jama’a, za mu tabbatar da gudanar da zaben kananan hukumomi cikin ‘yanci da adalci a cikin wannan shekara.”

Ya ce, a wani bangare na tsarin dimokaradiyyar gwamnatin da NNPP ke yi a jihar, shi ne yadda ta baiwa daukacin shugabannin jam’iyyar APC na kananan hukumomin jihar damar gudanar da ayyukansu.

Advertisement

Dungurawa, ya godewa al’ummar jihar bisa goyon baya da addu’o’i da suka yi a baya da lokacin da kotun koli ta yanke hukuncin da ta tabbatar da Abba Kabir Yusuf a matsayin zababben Gwamnan Jihar Kano.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending