Connect with us

News

NIN-SIM: Masu Hulda Da Kamfanonin Sadarwa Sun Koka Kan Katse Layinsu Daga Tsarin Kira

Published

on

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN

 

A ranar Larabar da ta gabata ne wasu masu hulda da kamfanonin sadarwa suka nuna rashin jin dadinsu kan katse layinsu da kamfanonin sadarwa suka yi daga tsarin kiran waya, duk da cewa kuwa, sun bi umarnin alakanta lambarsu ta kasa (NIN) da layinsu na kiran waya (SIM).

Masu hulda da kamfanonin sun bayyana rashin jin dadin su ne a wata hira da suka yi da Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya, NAN a Legas.

Gwamnatin Tarayya Ta Gargaɗi Ƴan Najeriya Da Su Daina Tarawa Ƴan Bindiga Kuɗi

NAN ta ruwaito cewa, kamfanonin sadarwa a Nijeriya da suka hada da MTN, Airtel, da Globacom da dai sauransu, hukumar kula da harkokin sadarwa ta Nijeriya, NCC ta basu umurnin aiwatar da cikakkiyar dokar katse layi daga tsarin kiran waya ga duk wani layin da ba a alakanta shi da NIN ba ko kuma wadanda sun alakanta amma ba a iya tantance NIN din ba zuwa 28 ga watan Fabrairu, 2024.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending