News
Wata gobara ta tashi a sansanin ’yan gudun hijira da ke Maiduguri a Jihar Borno
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Wata gobara ta tashi a sansanin ’yan gudun hijira na Garkin Block da ke Maiduguri a Jihar Borno.
A cewar wani ganau, gobarar ta tashi ne da misalin karfe 5:00 na yammacin ranar Litinin.
Kaduna: Sojoji sun kuɓutar da mutum 16 da ƴanbindiga suka sace a Kajuru
Ya ce, cikin kankanin lokaci wutar ta bazu cikin sansanin, lamarin da ya haifar da firgici a tsakanin mazauna yankin.
Sai dai Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Jihar Borno (SEMA) ta ɗauki mataki kan lamarin, inda jami’an kashe gobara suka isa da misalin ƙarfe 5:25 na yamma domin kashe gobarar.
Har zuwa lokacin kammala wannan rahoto, ba a iya tantance girman barnar da gobarar ta yi ba, haka kuma, ba gano musabbabin tashin gobarar ba daga bangarorin da abin ya shafa ba.
Aminiya ta ruwaito cewa, sansanin ’yan gudun hijira na Garkin Block na nan a kan hanyar Madinatu da ke cikin birnin Maiduguri.
-
News3 days ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion7 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News3 days ago
Zaben 2027: INEC Ta Amince Da Atiku Abubakar, ‘Yan Takarar ADC 470
