News
Wata gobara ta tashi a sansanin ’yan gudun hijira da ke Maiduguri a Jihar Borno
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Wata gobara ta tashi a sansanin ’yan gudun hijira na Garkin Block da ke Maiduguri a Jihar Borno.
A cewar wani ganau, gobarar ta tashi ne da misalin karfe 5:00 na yammacin ranar Litinin.
Kaduna: Sojoji sun kuɓutar da mutum 16 da ƴanbindiga suka sace a Kajuru
Ya ce, cikin kankanin lokaci wutar ta bazu cikin sansanin, lamarin da ya haifar da firgici a tsakanin mazauna yankin.
Sai dai Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Jihar Borno (SEMA) ta ɗauki mataki kan lamarin, inda jami’an kashe gobara suka isa da misalin ƙarfe 5:25 na yamma domin kashe gobarar.
Har zuwa lokacin kammala wannan rahoto, ba a iya tantance girman barnar da gobarar ta yi ba, haka kuma, ba gano musabbabin tashin gobarar ba daga bangarorin da abin ya shafa ba.
Aminiya ta ruwaito cewa, sansanin ’yan gudun hijira na Garkin Block na nan a kan hanyar Madinatu da ke cikin birnin Maiduguri.
-
News19 hours ago
Jam’iyyar Labour Party Ta Yi Alkawarin Kafa Hukumar Kula Da Hayar Gidaje A Kano
-
News3 days ago
Shettima @60: Haƙurinsa, Biyayyarsa Sun Taimaka Wajen Ciyar Da Manufofin Shugaba Tinubu Gaba — Kwankwaso
-
News6 days ago
KANO:’Yan Mata Uku ’Yan Gida Ɗaya Sun Mutu A Kifewar kwale-kwale A Tiga
