Connect with us

News

An Cafke Wasu Mutane 3 Kan Satar Raguna 132 A Mashegu

Published

on

Spread the love

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

An cafke wasu mutane uku kan laifin satar raguna 132 a karamar hukumar Mashegu da ke Jihar Neja.

Leadership ta ruwaito cewa wadanda ake zargin dai sun hada da Mohammed Abdullahi Chumo mai shekaru 30, Aliyu Salihu mai shekaru 20 da kuma Arzika Ahmadu mai shekaru 25.

Advertisement

RIKICIN EL-RUFAI DA UBA: APC  ta dakatar da shugaban mata na jam’iyyar saboda ta goyi bayan El-Rufai

Kakakin rundunar ‘yansandan jihar, SP Wasiu Abiodun, ya ce wadanda ake zargin sun amsa laifin ne lokacin da aka yi musu tambayoyi.

Ya bayyana cewa sun hada baki tare da sace raguna 132 a unguwar Manigi da ke karamar hukumar Mashegu.

“Abin farin ciki, a ranar 14 ga watan Maris, 2024, mai ragunan da aka yi satar, ya hangi wani da raguna guda shida daga cikin wadanda aka sace yana kokarin sayar da su,” in ji Abiodun.

Advertisement

Ya bayyana cewa, nan take aka kama wanda ake zargin sannan ya jagoranci tawagar ‘yansanda zuwa kauyen Jimi inda suka boye sauran ragunan.

Daga baya rundunar ta cafke Aliyu da Arzika.

An mika su zuwa sashen binciken manyan laifuka na rundunar domin gudanar da bincike.

Advertisement

Kakakin ‘yansandan ya kara da cewa, an mayarwa da mai ragunan dabobbinsa.

Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *