News
Ta Kama Mijinta Mai Shekaru 40 Yana Lalata Da Ƴaƴan Cikinsu
DAGA MARYAM BASHIR MUSA
Wata kotun majistare da ke Ikeja babban birnin jihar Legas, a ranar Laraba, ta bayar da umarnin tsare magidancin a gidan yarin a Kirikiri bisa zargin lalata da ’ya’yansa mata biyu.
Mai Shari’a, Misis Bola Osunsanmi, ta ki sauraron wanda ake kara, ta dage shari’ar zuwa ranar 26 ga watan Yuni.
Mulkin Dimokaradiyya Koma Baya Ya Kawo Wa Yan Nigeria Ba Ci Gaba Ba —Shitu Marshall
Ta ce za ta saurari shawara daga Daraktan shigar da kara na kasa kafin wannan lokacin.
Kamfanin Dillacin Labaran Najeriya NAN ya bayyana cewa tun da farko, dan sanda mai gabatar da kara, ASP Raji Akeem, ya shaida wa kotun cewa a watan Satumba na 2021, matar wanda ake kara ta kama shi yana lalata da ’yarsu mai shekara bakwai.
Yayin da a watan Mayu, 2024, matar ta kara kama shi yana kokarin lalata da wata ’yar tasu mai shekaru biyar.
Abin da ya fusata ta, ta kai karar sa ga hukuma.
Mai gabatar da karar ya ce, wadannan laifuka sun saba wa sashe na 137 na dokar laifuka ta jihar Legas da aka inganta a 2015.
-
News5 days ago
ICPC Ta Yi Barazanar Daurin Shekaru 7 Ga Masu Yiwa Baki Rajistar NIN A Matsayin Yan Najeriya
-
News1 day ago
Jam’iyyar ADC Ta Yi Watsi Da Cire Ta Daga Rijista, Ta Sha Alwashin Kalubalantar Hukuncin Kotu
-
News6 days ago
Hayar Jirage Hadi Sirika Ya Dakko Daga Habasha Don Damfarar Yan Najeriya Da Sunan “Nigeria Air” — Shaida
