News
Wata Sabuwa: Har Yanzu Muna Yajin Aiki Har Sai An Samu Sanarwa – Ƙungiyoyin Kwadago
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Ana kyautata zaton nan gaba kungiyar kwadago ta janye yajin aiki da ta shiga don neman karin mafi karancin albashi.
Nan gaba ake sa ran kungiyar za ta sanar da matsayar da ta dauka kan karin albashin bayan wata yarjejeniya da cimma da gwamnati a zaman da suka yi a ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya.
Jaridun Najeriya: Abubuwa 10 Da Ya Kamata Ku Sani A Safiyar Wannan Ranar Talata
A safiyar Talata kungiyar ta sanar cewa za ta zauna da rassanta ta ji daga gare su, domin daukar matsaya kan wannan lamari.
Rahotanni na nuni da cewa Ana kyautata zaton janye yajin aikin ne bayan gwamnati ta amince ta kara mafi karancin albashin ya haura Naira dubu sittin da ta gabatar wa kungiyar kafin zaman.
Bangarorin sun yi ittifaki kan haka ne a zaman sirrin da suka gudanar a daren Litinin da kungiyar ta fara yajin aikin gama gari a fadin Najeriya.
Bayan ganawar bangarorin suka fitar sanarwar cimma matsaya da cewa, “Shugaban kasa a shirye yake da ya kara mafi karancin albashi daga N60,000.
“Bangarorin za su ci gaba da tattaunawa a kullum na tsawon mako guda domin cimma matsaya kan wannan lamari.
“Kungiyar kwadago za ta je ta tattauna da rassanta kan wannan tayi, domin cim ma matsaya.
“Babu wani ma’aikaci da za a gallaza wa saboda shiga yajin aikin.”
Da haka ake kyautata zaton kungiyar kwadago za ta sassauta yajin aikin nata.
Yajin aikin dai ya durkusar da harkokin gwamnati da na kamfanoni da sana’o’in dogaro da kai.
-
News5 days ago
ICPC Ta Yi Barazanar Daurin Shekaru 7 Ga Masu Yiwa Baki Rajistar NIN A Matsayin Yan Najeriya
-
News1 day ago
Jam’iyyar ADC Ta Yi Watsi Da Cire Ta Daga Rijista, Ta Sha Alwashin Kalubalantar Hukuncin Kotu
-
News6 days ago
Hayar Jirage Hadi Sirika Ya Dakko Daga Habasha Don Damfarar Yan Najeriya Da Sunan “Nigeria Air” — Shaida
