News
Tur Ka Tur Ka: Wata Mata Ta Kashe Ragon Laiya Da Muciya Saboda Yacinye Ƙullun Ƙosai.
DAGA MARYAM BASHIR MUSA
An tabbatar da mutuwar wani rago jim Kadan bayan kaisa asibiti ranga-ranga raii ga hannun Allah sakamakon shirga masa muciya har sau biyar ƙwa-ra-ra da uwargida tayi masa.
Wani ganau ya shaida Jaridar Nigeria Jounals cewa saboda yacinye mata ƙullun ƙosai da take sayarwa gaba ɗaya bayan ta shiga ban ɗaki.
Bugu da ƙari mijinta ya ƙalubalanceta na aladolene ta biyashi ragon laiyarshi daya shafe tsawon lokuta yana kiwo da nufin a bana shima zaiyi laiya saboda bai taɓa yi ba.
Anan take dai haniya yaso ya kaure, sai dai daga gefe an samu kwamitin sulhu domin gudanar da zama na gaggawa na ganin uwargidan ta biya mijinta ragonshi data aika lahira a dalilinta na cewa yacinye mata ɗan jarin da take tattalawa wato ƙullunta na ƙosai.
Lamarin ya farune da safiyar jiya juma’a (7/6/2024) a sabuwar Anguwa ta (Kogoro Zone2 Kofar Gayan Zariya Jihar Kaduna.
-
News6 days ago
ICPC Ta Yi Barazanar Daurin Shekaru 7 Ga Masu Yiwa Baki Rajistar NIN A Matsayin Yan Najeriya
-
News1 day ago
Jam’iyyar ADC Ta Yi Watsi Da Cire Ta Daga Rijista, Ta Sha Alwashin Kalubalantar Hukuncin Kotu
-
News6 days ago
Hayar Jirage Hadi Sirika Ya Dakko Daga Habasha Don Damfarar Yan Najeriya Da Sunan “Nigeria Air” — Shaida
