Connect with us

News

An Gudanar Da Zanga-Zangar Tsadar Rayuwa Da Rashin Tsaro Da Lalacewar Tattalin Arziki A Kano

Published

on

Hoton Kamfanin Bluelens Multimedia

DAGA SALIM MUHAMMAD AHMAD 

A safiyar yau ne gamayyar kungiyoyin matasa na cigaban alumma dake garin Chiranci Karamar Hukumar Kumbotso suka gudanar da tattaki hadi da addu’a a garin chiranci.

Advertisement

Matasan sun Fito cikin tsari dauke da kwalaye masu rubutu ma banbanta inda suke dagawa suna cewa bamu yarda ba bazamu yarda ba da auren jinsi, tsadar rayuwa, rashin tsaro da lalacewar tattalin arziki.

Ba za mu tafi yajin aiki ba idan muka cimma matsaya da gwamnatin Tarayya – Kungiyar ASUU

Gamayyar matasan sun gargadi wakilan su dake majalisar tarraya Sanata da da Majalisar wakilai da cewa kada su yarda su sahalewa wannan dokar, kusani mu kuke wakilta, kuma mu musulmai ne don haka wajibi ne ku kare mana hakkin mu.

Advertisement

Muna kira ga maigirma Gwamnan Kano, Gwamnan al’umma daya barranta jihar kano da yadda da wannan tsarin, muna rokon malaman mu da su cigaba da watsi da wannan alamari, muna bukatar Yan majalisun mu su yi sani cewa wayanda suke wakilta fa suna cikin kuncin rayuwa, ba tallafi ake bukata ba, ana neman chanji me dorewa don haka ayi duk abunda za ai a nemawa talaka saukin rayuwa.

 

Advertisement

 

Bluelens Multimedia

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending