News
Da DUMI-DUMI : INEC Ta Bayyana Okpebolo Na APC A Matsayin Wanda Ya Lashe Zaben Gwamnan Edo
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta bayyana Monday Okpebolo na jam’iyyar APC a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan jihar Edo aka gudanar a ranar Asabar 21 ga wata, 2024 mai cike da fafatuka.
Okpebholo, mai shekaru 54, ya samu kuri’u 291,667 inda ya doke Asue Ighodalo na jam’iyyar PDP wanda ya samu kuri’u 247,274 da Olumide Akpata na jam’iyyar Labour Party (LP) wanda ya zo na uku a zaben da kuri’u 22,761. Wasu ‘yan takara 14 ne suka fafata a kujerar amma sun samu kasa da ‘yan takara uku na kan gaba.
Akalla Mutane 33 Sun Mutu A Wani Wurin Hakar Ma’adanai A Birnin Tehran
Advertisements
